Friday, August 7, 2015

Me Ya Sa Muke Rubutu?
Wace Irin Gudummawa Muke Bukata?

Daga
Ado Ahmad Gidan Dabino
Shugaban Kamfanin Gidan Dabino International Nig. Ltd., Kano

An Gabatar Da Wannan Takarda a Bikin Cika Shekara Hamsin a Duniya na Farfesa Ibrahim Malumfashi da kuma Bikin Cika Shekara Tamanin da Biyar da Fara Rubutu Kagaggun Labarai na Hausa, Wanda Aka yi a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe, Jami’ar Jihar Kaduna, a Ranar 8 ga Watan Disamba, 2012.


Tsakure
‘Nakan ji dadi a duk lokacin da na zo wucewa na ga wani ko wata suna karanta abin da na rubuta a cikin littafi, nakan ji kamar babu ya ni a wannan lokaci, ba don komai ba sai don na cika buri na, wato na isar da sakon da nake so ya isa ga jama’a, wanda kuma shi ya sa nake rubutu’.

Gabatarwa

Wadannan kalamai su ne suke fitowa daga ruhina zuwa zuciyata daga nan kuma har bakina ya furtawa a lokacin da na fara buga littafi ya shiga kasuwa, wato In Da So Da Kauna na daya a shekara ta 1991, wanda ake sayar da shi Naira biyar kacal ga masu karatu. Ba ni da wani buri ko bukata da suka wuce haka a wannan lokaci. Lokaci ne na samartaka, wanda babu wani abu da yake damun rayuwa ta face abin da na sa a gaba in ga na cim ma burina. Babu tunanin samun kudi ko suna a cikin zuciyata a wancan lokacin, fatana kawai ciwon da ke cikin zuciyata in bayyana shi ga jama’a, wadanda ba su sami kansu a irin wannan yanayi ba kada su sake su shiga, in kuma tsautsayi ya kai su sun shiga to, ta wace hanya za su bi su fita.

Na bukaci gudummuwoyi da dama a wancan lokacin, wadannan gudummuwoyi sun hada da neman shawarwari da duba min littafin a gyara Hausar da rabe-raben kalmominta kasancewar farin shiga ne ni a lokacin, kuma na sha wuya sosai wajen zirga-zirga a cikin birnin Kano da kewayenta. Ba dare ba rana ina bisa kekena don zuwa wajen mutanen da na bai wa wannan littafi don su duba kuma su yi min gyare-gyare a cikinsa.

Zirga-zirga ta aure ni. Je-ka-ka-dawo ba a magana. Hakuri dole ya zama abokin zamana saboda na yi ta samun sabanin lokaci na kammala aikin dubawar daga wasu mutanen da na bai wa karantawa da yin gyaran littafin.

Amma da ya kasance a kullum hakuri muka zama abokai da shi sai na ga alfanun abin, domin ko yanzu (yau shekara ahirin da daya) in aka dauko littafin aka karanta ba za a ga gyare-gyare rakwacam ba kamar yadda marubutan yanzu suke barin gyara a cikin littattafansu, wanda ba wani abu ne yake kawo hakan ba face rashin hakuri da juriya wajen kai wa a duba littafin.

Taken mukalata shi ne Me Ya Sa Muke Rubutu? Wace Irin Gudummawa Muke Bukata? Wadannan tambayoyi guda biyu suna da amsoshin su, kuma na san kowa ya tashi bayar da amsa za a ji ya fadi gwargwadon fahimtarsa da kuma ra’ayinsa. Don haka in muka ce tambaya ce mai sauki ba mu yi kuskure ba. Domin in dai kai marubuci ne kana da amsar da za ka bayar.

Me Ya Sa Muke Rubutu?

Wannan tambaya tana iya zama mai saukin gaske ga duk marubuta tun da kowa da irin dalilin da ya sanya ya shiga fagen rubutu, don haka ra’ayi ko amsar wannan tambaya ma za su bambanta. Amma don ba na son arar bakin marubuta in ci musu albasa sai na je kai tsaye ga marubuta don in ji waka a bakin mai ita, wato su marubutan su gaya min da kansu daga wasu jihohi kamar Kano da Kaduna da Bauchi da Jigawa, na kuma yi musu tambaya kamar haka:

Salam. Ina rubuta wata takarda a kan rubutu da marubuta don haka nake son a ba ni wannan amsarzan yi amfani da ita, Me ya sa kuke rubutu? Wace gudummawa kuke bukata?

Marubuta goma sha uku, maza guda 4 da kuma mata guda 12 na aikawa wannan sakon, duk sun ba ni amsoshinsu, kuma cikin mabambantan ra’ayoyi, wasu sun yi daidai da junansu wajen amsar, wato ra’ayinsu ya zo daya. Sannan kuma kamar hadin baki babu wata amsa da na same ta da safe, duk lokacin da na sami sakonne da yamma ne, sun fara daga 4.18  zuwa 11.26 na dare, a ranar farko, haka kuma a sauran ranaikun, duk da yamma na same su. Ga amsoshin da suka rubuto min kamar haka:

Da farko dai ni na fara rubutu domin sha'awa, ina jin dadi kawai idan ina rubutu, lokaci guda kuma sai nake amfani da damar domin na wa'azantar cikin nishadi.
Nazir Adama Saleh, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 4.18 na yamma.

In muka dubi abin da Nazir Adam Saleh ya bayyana game da dalilinsa na fara yin rubutun littafi, za mu ga sha’awa ce kawai ta kai shi ba wani abu ba, sai kuma jin dadin yin rubutun, sannan kuma ya gane cewa ashe baiwar rubutun da yake da ita hanyar wa’azantarwa ce ta samu gare shi, wanda kuma har zai iya nishadantar da masu karatu.

Don fadakarwa da nishadantarwa da kuma akida.
Alawiyya Wada Isa, Kano ranar 10/11/2012, karfe 4.37 na yamma.

Malama Alawiyya Wada Isa kuwa don ta fadakar da al’ummrta ta nishadantar da kuma akida su suka jawo ta afka fagen rubuta littafi.

Ni dai ina yin rubutu don tallafa wa adabi da inganta al'ada da kuma ba wa mata gudummawa ta zamtakewa da mazajensu da kuma yadda za su yi girki mai kyau da tarbiyyar yaransu da hakuri da juriya da yin sana'a. Sannan shi Rubutu babbar cuta ce da ba shi da magani tilas sai ka yi shi muddin saboda Allah kake don karuwar jama’a ba don kudi ba.
               
Sadiya Garba Yakasai, Kano  ranar 10/11/2012, karfe 5.20 na yamma.

Sadiya Garba Yakasai ta lallabo da nata hujjojin shiga fagen rubutu ne saboda agaza wa adabi da al’ada da kuma bayar  da gudummawa ga ‘yan’uwanta mata don su iya girki don kada a dinga samun sabani tsakanin magidanta da matansu wajen abinci domin wasu matan ba suiya dafa abinci ba, da tarbiyyar yaransu da nuna hakuri da juriya a rayuwa da kuma son a dogara da sana’a, bn das a ido a kana bin hannun mutane.

Ina rubutu ne saboda girmama harshena.
       
Asama’u Lamido, Kaduna, ranar 10/11/2012, karfe 6.23 na yamma.

Asama’u Lamido, ra’ayinta ya bambanta da wasu don ta bayyana cewa harshenta da take girmamawa shi ne ya sa take rubutu.

Kishin harshe na da yada al'adata, sannan na isar da sakona na fadakarwa cikin nishadi.
Rabi Talle Maifata, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 7.21 na dare.

Ita ma Rabi Talle Maifata sun hada hanya da Asma’u Lamido, inda ta nuna kishin harshen Hausa ne ya ya tsoma ta a tekun rubutu, sannan ta kara da son yada al’ada da fadakarwa hard a nishadantarwa.

Dalilin da ya sa ake rubutu yana da yawa, daga ciki akwai: Ilmantarwa da nishadantarwa da neman suna da neman kudi da sha'awar rubutu da soyayya da sauransu.
Umma adamu, Hadeja, ranar 10/11/2012, karfe 7.52 na dare.

Umma Adamu Hadeja ta hado abubuwa da yawa da take ganin suna sawa a shiga rubutu, wadanda suka kunshi ilmantarwa da nishadantarwa da neman suna da neman kudi da sha’awar rubutun shi kansa da kuma soyayya.

Muna rubutu don fadakarwa da nishadantarwa da nema wa al'umma mafita a al'amuran yau da kullum, kamar zamantakewa da neman ilimi da gyaran halaye da sauransu.
Bilkisu Yusuf Ali, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 8.39 na dare.

Ita kuwa Bilkisu Yusuf Ali, mun fahimci saboda ta nema wa al’umma mafita wajen al’amuran da suka shafi zamantakewa da gyaran halaye da neman ilmi da fadakarwa har ma da nishadantarwa, su ne suka kawo ta cikin farfajiyar yin rubutu. Kuma sun yi tarayya a wasu ra’ayoyin tare da Umma Adamu da wasu marubutan.

Ta hanyar rubutu nake sadar da sako ga dubban mutane ba tare da na yi tattaki zuwa inda suke ba.

Bala Anas Babinlata, Kano ranar 10/11/2012, karfe 8.52 na dare.

Bala Anas Babinlata, ya nuna don isa da sako ne, wanda rubutu yake isar wa wanda ba sai ya je kafa da kafa ba sakon sa yake isa ga jama’a.
Ni ina yin rubutu don na fadakar da kan al’umma game da zamansu, musamman aure da kishi da tarbiyyar yara.

Balaraba Ramat Yakubu, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 9.44 na dare.

Yaya babba kuwa wato Balaraba Ramat Yakubu, ta bayyana nata dalilan shiga taskar rubutu da cewa fadakar da al’umma wajen zamantakewa musamman ‘yan’uwanta mata a kan batun kishi da tarbiyyar ‘ya’yansu.

Babban abin da ya sa ni yin rubutu shi ne, kishin al'adunmu da kokarin fadakarwa da ciyar da yarenmu na Hausa gaba. Sha'awar rubutu ta karfafa a zuciyata ganin cewa hanya ce ta watsa manufofi, ta saukakakkiyar hanya, kuma mutum zai iya yin gargadi da wa'azantarwa da dora mutane a kan kyakkyawar hanya, walau ta hanyar tsoratarwa ko nishadantarwa. Wadannan dalilai su suka dasa min sha'awar rubutu. Don wani lokacin marubuci har kankanba yake yi, ya shiga rigar malamai ta hanyar wa'azantarwa. Kuma yin rubutu hanya ce ta kaifafa kwakwalwa, shi ya sa a duk inda marubuci yake za ka gan shi tamkar tsuntsun da yake yawo a sama, da zarar ya hango kuskure a kasa sai ya zaro biro da takarda ya shiga tunanin hanyar warware matsalar ta ruwan sanyi, yadda al'umma makaranta za su gano bakin zaren. Duk wadannan abubuwan su suke ba ni sha'awa a harkar rubutu.
Lubabatu Ya’u Babura, Kano, ranar 10/11/2012, 10.01 na dare.

Lababatu Ya’u Babura, ta dada karfafa ra’ayoyin da wasu suka bayyana cewa kishin harshen Hausa da al’adu suka sagalo ta zuwa farfajiyar fasiha, marubuta don ta ba da tata gudummawar, kuma ta kara da cewa shi rubutu hanya ce sassauka ta yada manufa ga jama’a, sannan ta nuna marubuta ma suna tarayya da malamai wajen wa’azi ga jama’a ta hanyar rubutunsu. Wadannan da ma wasu dalilan su ne suka jagorarta ta ci gaba da rubutwa da bugawa, jama’a suna karantawa.

Na fara rubutu da nufin gyara yadda wasu marubuta suka kalli mace da alkalaminsu, nufin ya fadada zuwa sakonni mabambanta.

Rahma Abdul Majid, Minna, ranar 10/11/2012, karfe 10.06 na dare.

Rahma Abdul Majid, ta sirnano nata jawabin ne da cewa, marubuta suna kallon mace da alkaminsu a baibai, shi ya sa ita kuma ta shigo don ta rubuta su daidai, a daina kallon mata a baibai kamar yadda wasu ‘yan’uwanta marubutan suka rattaba a littattafansu, daga wannan niyya kuma sai abubuwan suka fadada suka yi rasa har take rubutu na’u’i daban daban har da na masu aikata laifuka

Yana daga dalilan rubutuna, tsintar baiwar rubutun da na yi a tare da ni. Ka ga ya zama wajibi. Raba dannin jigo kuma sun hada da; bayyana abin da ke cikin zuciya da fadakarwa da tallar harshe da kuma neman kudi.

Aminu Abubakar Ladan (ALA), Kano, ranar 10/11/2012, karfe 11.26 na dare.

Shi kuma mai rumbun kalmomi, mahirun waka, Aminu Abubakar Ladan (ALA), ya ce tsintar biwar rubutun ya yi a tare da shi kawai don haka ya zama wajibi ya yi. Sai kuma ya kawo wasu raba-danni ko kananan jigogi na musabbabin yin rubutun, inda ya bayyana cewa fitar da abin da ke cikin zuciya da fadakarwa da da tallar harshe da kuma neman kudi.

Ni mai son isar da sako ga al’umma ce, sai na zabi hanyar rubutu wajen kai sakon.

Jamila Adamu Yaro, Bauchi, ranar 11/11/2012, karfe 2.41 na yamma.

‘Yar mutan Bauchi kuwa, Jamila Adamu Yaro ta nuna tuni take da son isar da sako ga jama’a amma sai ta zabi hanyar rubutu wajen isar das akon.

Ina rubutu ne don isar da sako tare da ilmantar da mutane da wayar musu da kai.

Adamun Adamawa, Bauchi, ranar 12/11/2012, karfe 2.50 na yamma.

Dan mutan Adamu, wato Adamun Adamawa ya bi hanya guda da Jamila Adamu yaro, da ma kuma dukkansu suna jihar Bauchi a yanzu, shi ma dai son isar da sakon ne ya ingiza shi cikin harkar rubutu.

Ina rubutu ne domin na isar das ako ga jama’a ta yadda za su rike aure da zumunci da zama da kishiya da sauran mu’amalar yau da gobe.

Aisha Abdulhamid Alhaji (Lawash), Bauchi, 25/11/2012, 9.20, dare.

Ina rubutu saboda yada harshena da al’adunmu na Hausa da fadakarwa da nishadantarwa ga masu karatu da kuma wayar da kan jama’a dangane da zamantakewar yau da kullum musamman auratayya wadda take jigon rayuwa

Sa’adatu Saminu Kankiya, 26/11/2012, 10.37, dare.

Idan muka lura da ire-iren dalilan da marubutan suka bayyana na abubuwan da suka sanya suka shiga fagen rubutu, za mu ga mafi yawa don son gyaran tarbiyyaar al’umma ne ba don neman kudi ba. Kuma dukkanin maubutan da na aika wa da  rubutaccen sakon (SMS) sai da na kira wayarsu muka yi magana baki da baiki, wasu sun ce in rubuta abin da suka fada min da bakinsu, amma na ce a’a, su aiko min a rubuce kamar yadda na aika musu a rubuce, don gudun idan gaya min aka yi da baki kila in rubuta abin da ba haka marubutan suke fadi ba, amma ta hanyar SMS, ba za a sami wannan sabanin ba. Kuma hakan aka yi suka rubuto da hannunsu.

Wace Irin Gudummawa Muke Bukata?

Game da wannan batu na abubuwan da marubuta suke bukata ta fannin gudummawa a wannan harka ta rubutu, ita ma amsar a bayyane take, kuma ba wuya gare ta ba, tun da duk marubuta sababbi da tsofaffi (na Hausa) sun san matsalar da marubuta suke fuskanta a fagen rubuce-rubuce da inganta shi da buga shi da tallata shi da sama masa tagomashi a wasu wurare, don haka da an tambayi marubuci kila zai fadi wannan miki da ya dade a zuciyarsa cikin hanzari. Ga abubuwan da marubutan suke ce:

Asamau Lamido, Kaduna:
Gudummawar da nake so, a sa mana ido a kan dillalan da ke safarar littattafai, suna cika riba kuma ba su da alkawari wajen biyan kudin littattafanmu.

Sadiya Garba Yakasai, Kano:
Muna mutukar son taimakon gwamnati ta san da mu marubuta, ta rinka tallafa mana, kuma muna bukatar manyan marubuta irin ku kuna yi mana gyara da sa mu a hanyar da za mu inganta rubutunmu, mu ma duniya ta san da mu, idan rubutu ba inganci tamkar shan shayi ne ba madara ko sukari. Ina son na ga ana yi mana gyara, ana kula da abin da muke yi, saboda ita rayuwa in har ba ka da mafadi, to, ba za ka ga da kyau ba, ina jin ciwon yadda manyan marubuta irin ku kuka bar mu kara zube babu mai sa mu ko hana mu, muna bukatar tallafin ku don bunkasa harkar.

Alawiyya Wada Isa, Kano:
Muna bukatar jagora na gari wanda zai tsaya mana a kan al’amuranmu, da kuma tallafawar gwamnati.

Nazir Adama Saleh, Kano:
Taimakon da muke bukata shi ne, mu sami hanyar da za ake yi mana dab'i mai inganci, sannan muna bukatar kara samun karfin gwiwa da kuma kauna daga gwamnati, ba tsangwama ba.”
 
Bilkisu Yusuf Ali, Kano:
Muna bukatar samun shugabanni tsayayyu da shigowar hukuma inda za ake hukunta wanda ya karya doka, kuma muna bukatar a sami wani ko kungiya ko kuma kamfani karbabbe wanda zai zama yana duba littafi wanda kuma in ya duban littafn zai sami yarda gun kowa, har malaman jami’a, sannan muna son littattafan ake nazarin su a matakinkaratu kowane.

Rahma Abdul Majid, Minna:
Bukatata ita ce a fahimci sakona.

Umma Adamu Hadeja, Jigawa:
Tallafin da marubuci ke bukata a wajen masu kudi da gwamnati shi ne jari da agaji da bashi. Sai kuma ingantaccen aiki da rikon amana da cika alkawari daga ma'aikatan madaba'a.”

Aminu Abubakar Ladan (ALA):
Muna bukatar goyon bayan hukuma da mazhabobin ilimi.

Adamun Adamawa, Bauchi:
Tallafin yada rubutun da yayata shi, shi ne bukatata.

Jamila Adamu Yaro, Bauchi:
Gudummawar da nake bukata ta kudi ce (hahaha).

Balaraba Ramat Yakubu, Kano:
Ina bukatar taimako ta kowace hanya a kan rubutu, kudi don buga littafin, ko kayan aikin bugawa, kuma hukumar ilmi ta tallafa  ta sa littattafan a manhajar karatu don mu fadakar da yaranmu”

Rabi Talle Maifata, Kano:
Gangamin wayar da kan marubuta daga lokaci zuwa lokaci. Iyaye su gane ba tarbiyyar yara muke batawa ba. Su karanta littafinmu kafin su yi hukunci a kanmu. A sanya littattafanmu a manhaja domin kada a manta da al’adunmu, amma littattafan da suke sun danganci hakan.

Lubabatu Ya’u Babura, Kano:
Hakika marubuta suna neman dauki ta hanyar a taimaka musu da kudade ko da rance ne don farfado da harkar rubutu, kuma yana da kyau a ce gwamnati ta samar da injinan dab'i ingantattu. Sannan a yi kokarin wayar wa da marubutanmu kai ta yadda marubuci zai bazama ya karo ilimi. Inganta shawarwari a tsakaninmu don kamo bakin zaren a kan abin da ya tabarbara harkar kasuwar littafi. Samar da wani fili a yanar gizo (internet) domin tallata hajar fasahar rubutun zube. Kana manyan marubutan da suka fara kawo salon rubutun da a yanzu aka fi raja'a a kan sa, su rinka jan mu kananan marubuta suna dada tunasar da mu irin nauyin da yake kan marubuci. Da darfafa gwiwar su ringa zurfafa tunaninsu ta hanyar zakulo matsalolin da suka addabi al'umma a rinka rubutu a kai, ba wai sai na soyayya ba. Manyan namu kuwa su ne irin su Dr. Yusif Adamu da Ado Ahmad Gidan Dabino da Bala Anas babinlata da Hajiya Balaraba Ramat da sauransu. Abu na gaba kuma shi ne sama wa marubuta kariya wajen yada manufofinsu.”      

Sa’adatu Saminu Kankiya, Katsina:
Taimakon da nake ganin muna bukata shi ne, na farko hadin kan mu marubuta, sai kuma samun jagoranci nagari da kuma tallafi daga hukumomi da kunguyoyi ta yadda za mu iya tsayawa da kafafuwanmu, ba tare da mun dogara ga ‘yan kasuwa ba. Kusan wannan ita ce babbar matsalar marubuta a wannan lokacin, saboda har yanzu ban taba jin wata kungiya ko hukuma da ta taba ba da tallafi ga sana'armu ba.

Tun da mun ji bayanai daga bakin marubuta ta hanyar rubutaccen sakon wayar hannu (SMS), ya kamata kuma a ji ta bakin zabiyar, wato shi mai rubuta wannan takardar, domin kila shi ma yana da nasa ra’ayin, wanda tun a farkon wannan takarda ya fara furtawa a cikin gabatarwarsa ta wannan takarda.

Ga ra’ayin mai gabatar da wannan takarda kamar haka:
Ni ina rubutu ne saboda ya zama jinin jikina kuma ya zama abokin rayuwata, wanda babu garin Allah da zai waye ban yi rubutu ba ko kuma na duba na wani na yi gyara ko ba da shawara ba, tun da ya zama aikina kuma sana’ata, ba ni da wani aiki da ya wuce rubutu da wallafa.

Gudummawar da ake bukata a harkar rubuta, akwai batun tsayayyiyar kungiyar marubuta wadda za ta kare hakkokinsu da nema musu daraja da kima a idon duniya. Kungiyar da za ta dinga kimanta harshen gida fiye da bakon harshe, wadda za ta dinga nema wa marubuta hanyoyin samun tallafi na sana’arsu, a wajen gwamnati ko masu hannu da shuni ko sha’awar rubutu ko kungiyoyi masu zaman kansu ko bankuna, a cikin gida da wajen Nijeriya, don bunkasa hanyoyin rubuce-rubuce musamman na Hausa. Wadda za ta nemo hanyoyin sanya gasanni don zaburar da marubuta su yi rubuce-rubuce masu inganci da nagarta da shirya taruka don kara musu sani da koyar da su dabaru na harkokin rubutu.

Mun ji ra’ayoyin masu ruwa da tsaki na ma’aikatar rubuta da wallafa, game da abubuwan da suka sa su suka tsunduma cikin rubuce-rubuce da kuma ire-iren gudummawa da suke bukata don bunkasa wannan sana’a tasu ta rubutu da wallafa. A duba kasa an takaita wadannan ra’ayoyi zuwa kasha hudu, kuma za a ga isar da sakon fadakarwa shi ne a kan gaba a zukatan marubuta daga nan sai girmama harshe da yada al’ada sannan batun neman kudi da a sha’awa su ne suke kafada da kafada da juna.

In muka dawo kuma batun irin gudummawar da narubuta suke bukata za  mu ga cewa batun samun tallafi daga gwamnati da hukumomi ne ya baibaiye wannan faifai na bayyana ra’ayi ko kididdiga sai kuma batun samun jagoranci yake biye masa sannan batun dillanci da dab’I ya zo na uku, sai abu na hudu batun kudI, wato taimako ko aro ko jari.

Kila yanzu daga wadannan bayanai da aka samu an gane ko kuma an soma gane su wane ne marubutan Hausa kuma don me suke rubutu, amma na san wasu a da can kafin su ji ta bakinsu suna ba su wata fassara ta daban, wato kila a ce don neman kudi ko bata tarbiyya suke yi, amma kila wadannan bayanai da aka ji daga gare su zai sa wasu su sauya tunani game da marubutan Hausa musamman na adabin zamani. Masu iya magana suna cewa, hange ba ya kawo nesa kusa, kuma ba ka gane mutum kila sai ka zauna da shi ko ka ji kalamansa.

A cikin watan Nuwamba na shekarar 2004, Shaihin Malami, Farfesa Graham Furniss ya ziyarci jihar Kano a Nijeriya daga London don ya yi hira da wasu marubuta na adabin zamani inda ya tattauna da su ya ji ra’ayoyinsu da kuma dalilan fara yin rubuce-rubucensu, wannan kuma ya sa ya gabatar da takarda wadda za a buga a cikin: Research in African literatures Vol. 43 No. 4, 2012. Takardar tana da shafuka sama da ashirin, kacokan ya mayar da hankali ne a kan wasu daga cikin ‘ya’yan kungiyar marubuta ta Raina Kama, kamar Badamasi Shaaibu Birji da Alkhamis D. Bature da Amina Abdu Na’inna da Dan’azumi Baba da Balaraba Ramat da kuma Ado Ahmaad. Wadannan mutane sun yi dogayen bayanai game da dalilai da manufofin yin rubutunsu da kuma matsaloli da suke fuskanta a wancan lokaci, yau kimanin sheakara takwas kenan, kum har yanzu wasu daga cikin matsalolin da suka bayyana ba su sauya ba sai ma karuwa da suka yi. Ga wadanda Allah ya sa suka karanta wannan takarda za su ga cikakkun bayanai

Kammalawa
An yi kokarin bayyana ra’ayoyin wasu daga cikin marubuta maza da mata daga jihohin Katsina da Kano da Kaduna da Bauchi da Neja da Jigawa maa hudu mata goma sha uku, wadanda suka bayyana dalilan da suka sa suka shiga farfajiyar rubuta littattafai da kuma ire-iren gudummawar da suke bukata don inganta wannan sana’a tasu ta rubutu da kuma neman a samar da wata hadaddiyar kungiya ta marubuta harsunan gida musamman ma Hausa don ta dinga samar wa da marubuta hanyoyin da a su inganta ayyukansu da sama musu tallafi da kara musu ilmi a bisa wannan sana’a.  


Manazarta

Furniss, Graham da Adamu A.U (2012) “Go by Appearances at Your Peril”: The Raina Kama Writers’ Association in Kano, Nigeria, Carving out a Place for the “Popular” in the Hausa Literary Landscape” Research in African literatures Vol. 43 No. 4, 2012 (forthcoming)


Sakonnin Wayar Hannu (SMS) da Aka Samu Daga Marubuta Don Amsa Tambayoyin da Aka yi Musu:

Nazir Adama Saleh, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 4.18 na yamma.

Alawiyya Wada Isa, Kano ranar 10/11/2012, karfe 4.37 na yamma.

Sadiya Garba Yakasai, Kano  ranar 10/11/2012, karfe 5.20 na yamma.

Asama’u Lamido, Kaduna, ranar 10/11/2012, karfe 6.23 na yamma.

Rabi Talle Maifata, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 7.21 na dare.

Umma adamu, Hadeja, ranar 10/11/2012, karfe 7.52 na dare.

Bilkisu Yusuf Ali, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 8.39 na dare.

Bala Anas Babinlata, Kano ranar 10/11/2012, karfe 8.52 na dare.

Balaraba Ramat Yakubu, Kano, ranar 10/11/2012, karfe 9.44 na dare.

Lubabatu Ya’u Babura, Kano, ranar 10/11/2012, 10.01 na dare.

Rahma Abdul Majid, Minna, ranar 10/11/2012, karfe 10.06 na dare.

Aminu Abubakar Ladan (ALA), Kano, ranar 10/11/2012, karfe 11.26 na dare.

Jamila Adamu Yaro, Bauchi, ranar 11/11/2012, karfe 2.41 na yamma.

Adamun Adamawa, Bauchi, ranar 12/11/2012, karfe 2.50 na yamma.

Aisha Abdulhamid Alhaji (Lawash), Bauchi, 25/11/2012, 9.20, dare.

Sa’adatu Saminu Kankiya, Katsina, 26/11/2012, 10.37, dare.



Tuesday, August 4, 2015

Forthcoming Book

Forthcoming Book 


University of Cologne – Department of African Studies

Seminar: Hausa Literature – “Magana Jari Ce“ (WS 10/11)
Lecturer: Hannelore Vögele
Speaker: Rebecca Roemer
Year: 2011
“The Soul of My Heart” by Ado Ahmad Gidan Dabino
Classical Hausa-Literature
Content
Central Topics:
• Reputation
• Relationships
◦ Friendship
◦ Family
• Love
• Marriage (in those days, before 1990 and nowadays, after 1990)
Summaya who comes from a good family falls in love with Muhammed, who is as much good educated as she is, but from a less rich family. She takes the initiative and writes him a loveletter. At first he rejects her, because he sees no chance for love between two people coming from a different status. She asks for a personal appointment to get the chance to convice him to become a couple.
And she succeeds.
At a wedding Sumayya gets to know the exceedingly rich young Abdulkadir. He as well had an excellent education, but he dropped to get involved into his father's business. She chats with him, but lets him know that she is already espoused to somebody else.
After romancing her unsuccessfully, Abdulkadir contacts Sumayya's Grandmother. Because the grandmother regards Abdulkadir as the perfect husband for her niece, she involves a witchdoctor.
However Muhammed is thinking of finishing the relationship.
Meanwhile Sumayya's Grandmother and Abdulkadir are fixing an appointment for the wedding, Sumayya and Muhammed are suffering more and more because of this situation.
Then Muhammed decides to go to Kaduna. Hereon Sumayya is on the verge of commiting suicide.
In Kaduna Muhammad gets to know Najahatu. At the same time Sumayya is writing her suicide note to her beloved one. He is also on her mind while she jumps into the river to kill herself.
But Sumayya is rescued by some passengers and brought into hospital immediately.
Because she lost a lot of blood both Muhammed and Abdulkadir donate blood to her.
By now Muhammed's mother supports and affirms their love. Even Sumayya's parents believe in the love of the couple and consult with friends. Only Sumayya's grandmother is not assuring herself and involves a witchdoctor again. At the hospital, Sumayya tells everything to her nurse Saratu, who falls in love with him expeditiously.
Shortly after Sumayya are officially engaged, Najahatu from Kaduna visits him surprisingly. It finally comes to a confrontation: While Najahatu tries to seduce him, Sumayya comes home and moreover Saratu, the nurse appears.
But the whole situation is claryfied and Sumayya forgives Muhammed. So they marry. Their wedding is considered as a historical moment. Allah and Islam play a very important role.
The witchdoctor is a permanet guest of the grandmother. Sumayya records the grandmothers' evilness secretly and plays it to her father. Thereupon the grandmother leaves the family and everybody feels relieved.
The story has a tragic end for Abdulkadir. On his way back with his father from a businesstrip, his father is shot down. Abdulkadir himself is hit so strong that his arm is rotten. At the same time he is robbed so that he is bankrupt.
The story ends in a monologue which includes so to say a morale.
• Morale of the story:
“Slow and steady they say, wins the race. […] One should not harbour illwill against
anybody. It might easily rebound back”.
• An interesting point is the author's choice of names for the characters:
◦ Muhammad, Mohammed - Praised, praiseworthy; the name of the Prophet
◦ Sumaiyah, Sumayyah - Name of a lady companion of the Prophet; the first martyr in Islam
◦ Abdul, Abdel, 'Abd al - Servant (of Allah)
◦ Kadir - Powerful
◦ Najah, Najaah - Success
◦ Sarah - Name of the wife of the Prophet Ibrahim
The Author
• Ado Ahmad Gidan Dabino *1964 in Kano
• Attended Bayero University Kano
• His work:
14 books (11 novels in Hausa, 1 biography and 2 have been translated into English)
In Da So Da Kauna 1 & 2 = The Soul of My Heart
Masoyan Zamani 1 & 2 = Nemesis
Hattara Dai Masoya 1 & 2
Wani Hanin Ga Allah… 1 & 2
Duniya Sai Sannu!
Kaico!
Zalimu (hausa theatre)
Sarkin Ban Kano Alhaji Dr. Muktar Adnan (biography)
• One of the founders and vice president of the Association of Nigerian Authors (ANA)
Kano State Branch
• Chief of Gidan Dabino International Migration Limited
• Won Noma Award for Publishing in African (UK)
• Writes for daily newspapers and magazines and all over in Nigeria he gave seminars
and workshops
• He writes when he's in the mood for it. There are no specific, fixed times for writing.
Writing can happen any where, any time.
• He was the main actor of his in 1996 pictureized book „In Da So Da Kauna“ (The Soul of My Heart). Moreover, since 1996 he has been the Producer/Director of several Hausa Movies
• Hobbies: Travelling, research, writing
• Presently, he's working on a new book
◦ Content: „Rabuwa (Separation) [his] love true life story. It's about his travelling to
Europe – Germany, Italy, France and GB
◦ Title: “Gani Da Ido… (Seeing is Believing)“
• Ado Ahmad about African Literature:
“To me, African literature is a reliable tool for educating the world about the beauty of African culture, history and tradition as well as its people. Equally important to add is the fact that no society would developed without a striving literature, hence I see African literature as a vehicle for African future transformation and prosperity”.
• Ado Ahmad about the Nigerian Press:
“On Nigerian press, I always have mixed feelings about the role they have been playing. True, the Nigerian press could be said to be one of the most vibrant Press in the world especially going by the historical role they played in the fighting colonialism, ending military dictatorship and institutionalization of democracy in my country, etc. But sadly, in spite the aforesaid important role the Nigerian press, yet I am fully convinced that any critical mind cannot completely exonerate our press from sharing the blame of Nigeria’s misfortune, especially in terms of watering the seed of polarity in Nigeria. It is disturbing to note that Nigerian press do polirazed Nigerians along ethnic, religious and sectional lines”.
• Ado Ahmad about his first book:
“My first novel is called In Da So Da Kauna (The Soul of my Heart). It is not for me to say whether the subject of my book (The Soul of my Heart) has radically changed its readers’ behaviors, but what I cannot deny is the fact that the book was well received among the reading public as well as influenced some of the readers to pick their pens too. And with all humility, I could say in terms of promoting reading culture among the Hausas my books and that of other Hausa writers have succeeded in keeping the light of reading culture alive”.
Quellen
• http://gidandabino.blogspot.com/ (08.01.11-17:55, 16.01.11-19:32, 30.01.11-12:00)
• www.facebook.com
• Interview January 2011
• „The Soul of My Heart“, Ado Ahmad Gidan Dabino, Gidan Dabino Publishers, 1991
• Informations about the names:
Muhammad, Mohammed (http://www.sudairy.com/arabic/masc.html#M(30.01.11 –
15:16))
Sumaiyah, Sumayyah (http://www.sudairy.com/arabic/fem.html#S (30.01.11 – 15:18))
Abdul, Abdel, 'Abd al (http://www.sudairy.com/arabic/masc.html (30.01.11 – 15:28))
Kadir (http://www.mybaby.net.au/index1.php (30.01.11 – 15:33))
Najah, Najaah (http://www.sudairy.com/arabic/fem.html#N (31.01.11 – 22:55))

Thursday, July 9, 2015

Gidan Dabino as an Intellectual and International Icon
(Gwagwarmayar Ado Ahmad Tsakanin Manyan Manazartan Duniya)

Prof. Dr. Abdalla Uba Adamu
Department of Mass Communication
Bayero University, Kano

Perhaps we should start with trying to understand the key variables associated with this talk: intellectual, and international.  The latter concept, international, is straight-forward enough, because it connotes a straddling of nations and going beyond a specific national barrier. Let me therefore focus my definition of term therefore on the former concept, ‘intellectual’.

In human societies, the Intellectual is the man or woman dedicated to critical thought (study, introspection, and reflexion) about the reality of society; who communicates the derived ideas towards the resolution of society’s normative problems (social, political, and cultural), and so derives authority in the public sphere. Coming from the world of culture, either as a creator or as a mediator, the Intellectual participates in the world of politics, either to defend a concrete proposition or to denounce an injustice, usually by producing or by extending an ideology, and by defending one or another system of values.

In our times, the term “Intellectual” acquired positive connotations of social prestige derived from the person being a man or woman possessed of intellect and superior intelligence, especially when his or her activities in the public sphere exerted positive consequences upon the common good, by means of moral responsibility, altruism, solidarity, in effort to elevate the intellectual understanding of the public at large, without manipulation, false populism, paternalism, or condescension.

The intellectual and the scholarly classes are related; the intellectual usually is not a teacher involved in the production of scholarship, but has an academic background, and works in a profession, practices an art, or a science. The intellectual person is a man or woman who applies critical thinking and reason in either a professional or a personal capacity, and so has authority in the public sphere of his or her society. Further, the term "Intellectual" identifies three types of person, one who:

is erudite, and develops abstract ideas and theories
a professional who produces cultural capital, as in philosophy, literary criticism, sociology, philosophy, medicine, science or
an artist who writes, composes, paints, etc.

Using these definitions and typologies, I want to look at the achievements of Mallam Ado Ahmad Gida Dabino as both an intellectual and international icon or figure.

Although Mallam Ado does not have academic higher degrees usually associated with modern intellectuals, nevertheless his achievements have attained the status of intellectual achievements regardless of the measuring instrument used. For one thing, and in common with all other intellectuals, he has a vision to excel. Other intellectuals in a similar situation in our society could include people like Abubakar Imam, Mallam Aminu Kano xxx.

Remarkable amongst his achievements as an intellectual is his grounding in the grassroots philosophy of the community he lives in. This community ethnography is what lends credence to his narrative prose about life and how to live it. Thus Mallam Ado’s business craft is located solidly and squarely with a local community of ‘ordinary’ people  who share his vision about intellectual literariness. His office has become a portal through which ideas move in and out. When I first started my own foray into literary analysis of contemporary Hausa literature, my first starting point was the Gidan Dabino Publishers’ office along Sabon Titi in August 1999 when I encountered him for the first time. Almost all those I asked to point out to me the starting point of mass culture in Hausa prose fiction would point to Mallam Ado—so I traced him in his office, introduced myself, and have remained with his office since then: in fact we have joint lease in the office block we are now.

Ado Ahmad is a writer, and there is nothing more intellectual than bringing down abstraction to a concrete level where people can grasp often the absurdity of the abstract. Being a writer gives Ado Ahmad opportunities to create vistas of literary landscapes that captures the imaginations of thousands of people—often as in the case of many later notable writers, bringing them into the literary fold. The famous writer, Rahama AbdulMajid, is a case in point when she explained that she became motivated to become a writer due to Ado Ahmad’s novels being read over the radio.

Ado Ahmad pioneered the transition from the literary to visual medium when he adapted his famous novel, In Da So Da Kauna, into a video film version, thus providing an intellectual template to the then developing Hausa film industry. Other intellectuals such as Ms. Balaraba Ramat Yakubu, Bala Anas Babinlata, Alkhamees Bature Makwarari, Sunusi Shehu Burhan, Ado Mohammed, all became literary adapters when they also converted their individual stories into the film media—experimenting not only in the craft of storytelling in different media, but also exercising their intellect in embellishing their narrative prose for the film medium.

The International Intellectual
The first and major international recognition for Ado Ahmad’s craft was in Niger Republic, particularly in the towns of MaraÉ—i, Damagaram and Niamey. In each of these cities, Ado’s name became a household name through his novels which were read over the radio. Things reached a head when Ado himself was invited to MaraÉ—i to anchor a series or radio programs and become a judge in literary competitions. No other Hausa writer, from which ever generation has ever attained this cross-border collaboration in literary circles.

Ado thus became a virtual ‘Nigeriene’ –though he still could not speak French!—and a celebrity, through his writings as well as special edition radio host programs. Soon enough, he has established a vast network of contact and collaborators in Niger Republic. This was amply demonstrated when in 2006 he led a whole convoy of writers and academicians on an international collaboration between the Kano Branch of Association for Nigerian Authors (ANA) of which he was the Chairman and Gashingo Publishers of Niamey under Dr. Mallam Garba Maman. Since then he had become a central figure in cross-border collaborations between Nigerians and NigĂ©riens in literary activities—creating ties and networks that diplomatic channels have not been able to forge.

This was just the beginning. For subsequent international activities of Ado Ahmad saw him as an invited guest or publishing collaborator for UNESCO to regional meetings in Mali, Niger, Benin Republic, Ethiopia, France and Italy. In each of these places, Ado Ahmad made strong and persistent presentations about indigenous writers in Africa, thus further promoting the cause of indigenous literary scholarship on a scale never done before by any contemporary writer.

And it did not stop there. I was a witness to Ado Ahmad’s internationalization when he went to Germany in 2010 to present a paper as a guest speaker at the Hamburg University. The place was packed full with mostly female students who listened to Ado’s present with rapt attention. He spoke in Hausa, but his speech was immediately translated into German.

Subsequently, Ado was also invited to the famous School of Oriental and African Studies, SOAS, University of London in the UK in 2011 to present another paper, as well as premier his film Sandar Kiwo. Again students and staff jammed the hall to listen to him—this time in English, for along the line in his career, Ado has been able to graduate from the Adult Education classes to a self-taught mode where he can fluently converse in English to anyone, anywhere.

While Ado has never been to Poland or India, his film Sandar Kiwo was also premiered in these countries, at the University of Warsaw, Poland; and in India, the film was shown by Blaft Publishers based in New Delhi, to a select group of Indian writers of pulp fiction.

By now we all know who, or what, the writer is. He or she is a poet, a playwright, an essayist and/or a novelist. But he or she is also the writer of the editorials and columns, the investigative and explanatory reports that are among the many forms journalism has developed in discharging its public task of describing and interpreting the human environments and humanity itself. In the digital age, the writer is also the blogger who makes it his concern to gather and provide information on issues of citizen concern and to comment on them online. Ado Ahmad is this and more. He is truly an international and intellectual icon, on a scale no indigenous Hausa writer in contemporary times has been able to attain. His Member of the Order of the Niger is well-deserved.

Here are testimonies from three of Ado’s friends and collaborators: Prof. Graham Furniss, from London, England, and the first person to study Hausa contemporary novels; Dr. Marius KraÅ›niewski from, Warsaw, Poland, and Dr. Carmen Mcain from Wisconsin, United States.

***

Comments from Prof. Graham Furniss, OBE, School of Oriental and African Studies, London, 20th October, 2014.

I see this award as recognition for the central role that Ado Ahmad Gidan Dabino has played in a remarkable African renaissance that sprang up from the grassroots. He was a central figure in the explosion of popular fiction and then video film in Hausa from the 1980s onwards. His positive, can-do attitude and his open and engaging personality drew many to him and to his writings. His writing touched young people's aspirations and hopes and reflected many of their experiences of life in difficult times. Articulate and witty, he was not afraid to take up any path that might lead him to greater achievements -- he has been a writer, a publisher, a radio host (including in Niger), a video film producer, and a friend to many.

I first encountered him in Kano when I was researching the rise of Hausa popular fiction and the activities of the Raina Kama writers' club where he was a founder member. Subsequently, I met him again when he visited London and the University here. I have to say that I was often asked by radio and television hosts in Nigeria whether popular fiction and video was of any value and whether it should have been banned. My reply has always been that it is the role of a researcher to document and analyze what is happening on the ground and it is for other authorities to pronounce on the value of differing forms of cultural production. Being aware that both books and films have come under attack in years past, this award comes as a major acknowledgement by the highest Nigerian state authorities of the importance and the value of these forms of artistic endeavor, and I can think of no one better to receive the honour on his own behalf, and on behalf of all the book writers and film makers that he has encouraged and supported, than Ado Ahmad Gidan Dabino,  MON.

***

Dr. Mariusz Kraśniewski, Polish Academy of Science, Warsaw, Poland, 20th October, 2014


The first time I’ve heard the name of Ado Ahmad Gidan Dabino few years ago when I was a PhD student at the University of Warsaw. We didn’t knew each other back then, his name appeared as a quite enigmatic signature on many of the books I’ve been using in my research. Gidan Dabino Publishers, Kano -  it was always the sign that guaranteed very high publishing and scholarly qualities of the works. Thus I can say that thanks to Ado Ahmad Gidan Dabino, the works of many prominent or promising Hausa scholars and authors (including Ado himself) were able to cross the borders between continents and provide to us, Polish students and scholars, the insight into academic life of Northern Nigeria. The insight that is so greatly needed as it brings different perspectives of the research while still maintaining high scholarly quality of methodology and research.

Few years later, during my stay in Kano, I’ve finally met Ado in person. I was not surprised to realize that he is not only the shark that sails confidently through the turbulent waters of the publishing industry, but above all, he is also a modest, kind and friendly person. On this occasion we were able to talk about  his work and future plans, but this meeting was important for me also for some other, more personal reasons. When, some weeks after our meeting,  I’ve lost my consciousness because of cerebral malaria, that was Ado who was the first person to confirm my identity as a visiting associate of the Bayero University.  I will be grateful for that ‘till the end of my life as his help was a vital asset that created the possibility for my friends from BUK  to organize the treatment and take care of me during my stay in the hospital.

Mallam Ado, I was very happy to hear from Professor Abdalla Uba Adamu that you’ve been honored with a national recognition of Member of the Order of the Niger (MON) by the President of Nigeria. I’d like to be here to personally shake your hand and tell you that the above-mentioned Order is a perfect gift for your 50th anniversary and that it is a well-earned addition to the long list of your achievements as a writer, scholar and social worker. I would like to sincerely congratulate you for this distinction and I am sending you as well my best wishes for your 50th birthday.

Allah ya ba Ka lafiya da alheri!

***

Dr. Carmen McCain, University of Wisconsin, Madison, United States, 25 October, 2014

I congratulate Ado Ahmad Gidan Dabino on receiving the national honour Member of the Order of the Niger. I’m delighted to see the national government recognize his achievements, as not only one of Nigeria’s bestselling Hausa authors but also an award-wining playwright, publisher, filmmaker, and important theorist of Hausa literature and culture.

Ado Ahmad Gidan Dabino is directly responsible for my decision to study Hausa literature and film and for my career so far. I had initially planned to study Hausa as a requirement of my PhD program at the University of Wisconsin, Madison, but to write my PhD thesis on English-language Nigerian literature. Reading Gidan Dabino’s In da So da Kauna in 2005, when studying advanced Hausa in Sokoto, changed my research and changed my life. I initially had a hard time reading Hausa. I read several of the Hausa “classics” almost half way through without understanding much of what I was reading. It was not until I began reading In da So da Kauna that I began to read quickly and hungrily, as I had read the fantasies and historical romances I had loved in high school, anxious to find out what would happen to the star-crossed lovers. It was out of this experience that I began to love reading Hausa novels and films and the rest is history. Ado Ahmad Gidan Dabino, as one of the leaders of the contemporary literary movement in Hausa, is important in helping bringing about a reading revolution in northern Nigeria. Northern Nigerians are reading more in Hausa than they are in English, and, in a country where intellectuals commonly complain about reading culture, that is a gigantic accomplishment. What I admire the most about Gidan Dabino’s writing is his brilliant dialogue, which captures the banter of every day life, and his ability to tell a story that holds the reader in suspense.

I am grateful to him for putting me on the path to scholarship, and I thank him for all the time he has spent in personally helping me with my research and introducing me to other writers.

Na gode, Ado. Na taya maka murna.

Carmen McCain (Talatu)

Thursday, October 9, 2014

Wednesday, October 8, 2014


l'm pleased to inform you that Nigeria has bestowed on me with national honour of Member of the Order of the Niger (MON) in recognition of my selfless service to public good and commendable contributions to Hausa literature, publishing and film industries. This success would not have been possible without your support and prayers. Thanks a lot.  


Tuesday, June 15, 2010

ZIYARA ITALIYA DA FARANSA: NA JE KALLO NA ZAMA ABIN KALLO

Sashen kula da ilmi na hukamar da ke kula da kasashe masu amfani da harsunan faransanci, wato OIF da ke kasar Faransa, wanda Waziri Amadu dan kasar Nijar yake jagoranta su ne suka shirya wannan tafiya.

A kashin farko na wannan tafiya, wasu kamfanonin wallafa guda biyar ne suka fara zuwa kasar Italy da Faransa daga kasar Nijar da kuma Afrika ta tsakaya, kwanaki biyar su ma a suka yi a tsakanin Faransa da Italiya.

Bayan sun koma kasashensu ne mu kuma muka je wannan ziyara, a wannan karon shugabannin kamfanoni wallafa littattafai uku ne suka je wannan ziyara, wato Dan bourgami Magaouata, shugaban kamfanin Danbourgami (Niger)da Issouf Oumarou Alzumma shugaban kamfani Alpha (Niger) sai kuma Ado Ahmad Gidan Dabino shugaban kamfanin International Nigeria Ltd. (NIGERIA).

Mutum biyu da suka taho daga Nijar sun riga ni zuwa da kwana biyu, ni na bar Nijeriya ranar Lahadi 8 ga watan 11 da dare misalin karfe goma sha daya in da muka wayi gari a birnin Paris wajen karfe shida muka sauka, wato mun yi kamar awa shida muna tafiya kenan.

Daga nan muka shiga layin da jami’an tsaro za su duba passport dinmu. A nan na ga abin mamaki da ban haushi wato fasfot din Nijeriya ba a daraja shi a kasashen duniya, domin ni kadai na ga an dade ana duba fasfot dina sannan aka nemi in nuna takardar gayyata da aka ba ni ta zuwa wannan ziyara a kasar Italiya kafin a buga min hatimi a kan fasfot dina, abin ya ba ni mamki har na shiga tambayar kaina da kaina, shin ta yaya shi wannan jami’in tsaro zai ce in kawo takardar gayyata ta ya gani, bayan ga biza a ba ni ta kasar Italiya, shin ofishin jakadanci Italiya zai ba ni biza ne ba tare da na cika sharudan da suka tanada ba? Wannan abu ya ba ni takaici kwarai da gaske, don ganin babu wanda aka yi wa wannan abu sai ni kadai dan Nijeriya. Amma babu yadda zan yi don na san wasu daga cikin ‘yan Nijeriyar ne suka zubar mana da kima da martabar da muke da ita a da, na san lokacin da in dan Nijeriya zai tafi Ingila ba ya bukatar biza sai in ya je filin jirgin saman London a nan za a buga masa hatimi ya shiga, kamar yadda in mutum zai shiga kasar Nijar yana da fasfot ake yi masa.

Haka dai muka wuce muka je wajen jiran wani jirgin da zai dauke mu zuwa kasar Italiya, Mun yi jira na wajen awa daya sannan muka sake shiga wani jirgin muka nufi Italiya. Nan kuma a cikin jirgin ni kadai ne bakar fata, duk jajaye ne daga Turawa sai mutanen kasar Sin da Indiyawa da Italiyawa da dai sauransu.

Bayan kamar awa biyu muna tafiya sannan muka sauka a kasar Italiya. A nan ban gamu da wata matsala ta duba fasfot ko wani abu ba, illa kawai jinkirin daukar babbar jakata da aka dan samu, don na fi minti talatin ban ga jakar ta iso daga ramin da ake turo kayan ba.

Tun lokacin da muka sauka daga jirgi na kira wayar shugaban tafiyar, wato Waziri Amadu, ya amsa min da cewa shi ma yanzu ya sauka, don haka yana nan yana jira na a wajen fita, na shaida masa ni kuma ina so in dauki kayana tukunna.

Da na ga kayan sai na sake kiransa na ce ga ni nan fitowa ina za mu hadu? Ya shaida min. Muka hadu muka hau tasi muka nufi masaukinmu. Tsakanin masaukin da filin jirgi ya kai nisan kilomita ashirin.

Bayan mun isa masauki ba mu fi minti goma sha biyar ba sai direban kamfanin da muka zo don ziyararsu wato Arti Grafiche ya zo ya dauke mu don ya kai mu kamfanin, domin su abokan tafiyar tamu da suka zo daga Nijar suna can kamfanin. A kan hanya ne direban yake shaida mana ai ya je filin jirgi don ya dauko mu ya kasa samun mu.

Bayan wasu ‘yan mintina muka isa kamfani Arti Grafiche da ke unguwar masana’antu ta Pomezia, muka iske Magawata Danbourgami da Umar Alzumma, daga nan muka ci gaba da tattaunawa game da abin da ya kawo mu, wato kulla huldar yin aiki tare a bangaren wallafa littattafai, a nan dai muka wuni a kamfanin, sai da yamma bayan karfe biyar sannan jami’ar kasuwanci ta wannan kamfani wato Ms Nelly ta dauke mu mu hudu ta kai masauki.

Washegari muka sake komawa kamfanin don ci gaba da tattauna batutuwan ayyukan wannan kamfani na wallafa littattafai. Abubuwan da muka tattauna shi ne batun farashi da kuma yadda in an buga littattafan za a debu su a jirgin ruwa ko na sama da kum sauran wasu batutuwa da suka shafi kulla hulladar aiki tare da su da mu da muka zo daga Afrika ta yamma.

Da lokacin cin abincin rana ya yi muka koma masaukinmu tare da manajar kasuwanci Ms Nelly. Daga baya kuma mutane biyu daga cikin manajojin kamfanin suka zo don mu ci abincin rana tare das u, wato Mr. Poulo da Mr Luciano. Gaskiya an baje kolin abinci amma kash! Irin wanda zan iya ci kadan ne a ciki, wato kamar biredi da kifi sai kuma nama, amma sauran sun gagare ni. Haka dai aka yi wannan cin abinci aka gama, amma in na kalli wani abincin sai in ji zuciyata na tashi saboda kwamacalar da aka hada a cikinsa. Lallai abincin wani ba na wani ba.

Bayan an gama muka sake dawowa kamfanin don mu ga injinan da ake buga littattafai na zamani. Mun dade a cikin wannan bangare na buga littattafai kuma mun ga injinan da ba mu taba gani ba sai dai a cikin mujallu ko a finafinai na Turai. A nan muka ga wani inji mai saurin buga littafi, wanda kafin awa guda zai buga madaidaicin littafi guda 10,000. Lallai aiki ga mai kare ka.

A rayuwar duk wani mai harkar buga littafi ya ga ya mallaki mada’a, haka shi kuma dan jarida ya ga ya kafa kamfanin mujalla ko jarida, mai harkar yada labarai na rediyo kuma ya ga ya kafa gidan rediyo ko talbijin. Haka dai muka fito muna ta addu’ar Allah ya gwada mana lokacin da za mu mallaki ire-iren wadannan kayan aiki na dab’in littattafai. Da yamma bayan karfe biyar aka dawo da mu masauki.

A wannan rana da dare ya yi muka tafi wani gidan cin abinci, ga katon littafi an kawo don mu zabi abincin da za mu ci amma da Italiyanci aka rubuta kuma Italiyanci suka iya sai Faransanci da Turanci dan kadan wanda ba a rasa ba. Ni dai na ce ina son a kawo min shinkafa da kifi, da yake yarinyar mai kawo abincin ta fi fahimtar Faransanci sai aka shiga yi min tafinta, wato fassara daga Hausa zuwa Faransanci ana gaya mata abubuwan da nake so, mai yi min tafinta ya gaya wa yarinyar irin abin da nake so na ci da kuma da sha.

Assha! An kuma mace ta haifi mace. Bayan mun yi zama fiye da minti talatin muna jiran abincin, tun da dama a lokacin da ka fadi abin da za a kawo maka sannan ake dafawa. Can aka kawo abinci, na kalli shinkafar da na ce a kawo min na kau da kai, don abubuwan da na ga an zubu a ciki, an yi dafa duka da su, wato kaguwa da dodon kudi da wasu abubuwa masu kafafu kamar gizogizo su ne aka yi wannan dafa dukar shinkafa da su. Nan fa na kama fada, cewa a gaya mata a garinsu haka ne shikafa da kifi, ai duk duniya kifa guda daya ne, ba kaguwa ko dodon kudi ne ba. Wani abin haushi dodon kodin har da kwanson sa (kokonsa) aka zubu shi turmis.

Mai yi min tafinta ya ce, ta koma ta kawo kifi da dankalin Turawa. Kuma abincin ga tsadar tsiya, kowane filet daya ya fi Naira dubu uku a kudin Nijeriya, ga shi kuma dan kadan, (ita dai wannan dafadukar da ba za ta ciyu a gare ni ba). Nan dai shugaban tafiyar tamu wato Waziri Amadou da yake mai barkwanci ne, sai ya ce, ‘Ai kuwa Malam Ado ya kamata ka ci ka ji ka ga sai ka rubuta a rubutun ka nan gaba ko?’ Na ce, ‘Ai in na ci wannan abubuwan ban san yadda za mu kare da su ba, maganin kada a ji kada a fara, don haka ba zan fara ba.

Washegari kuma muka tafi yawon ganin gari, inda direban kamfanin Arti Grafiche mai suna Alkabeer, wani dan kasar Marocco ya dauke mu ya nufi birnin Roma don mu ga toshon birnin Roma da kuma fadar Fafaroma da ke Batikan.

Nisan birnin Roma daga Pomezia wato inda muka sauka ya kai kilomita ashirin da biya. Muna dosowa kofar shiga birnin Alkabeer ya ce wannan ita ce kofar shiga birnin Roma.

Haka dai muka yi ta ganin gine-gine tsofaffi wadanda suka yi shekaru dubunnai kamar yadda ake shaida mana. A nan muka ga ginin da maza ke gwada karfi, wato fadar Siza na Roma, wato wajen da aka yi fim din nan na Giladiyeto.

Daga nan bayan mun gama da wadannan wuraren sai muka nufi fadar Batikan. Muna zuwa muka dinga ganin mutane masu kai ziyara don kallo, wato irin mu da kuma masu zuwa don yin ibada. Kofar shiga wajen ibadar akwai jami’an tsaro da motocinsu suna kai komo don tabbatar da wani abu bai faru ba. Tsofaffi da ba za su iya tafiya ba ana tura su a kan keken guragu, ga kuma masu cin kasuwa nan a wajen harabar suna ta karakaina.

Wani abin dariya da aka yi, mu muna daukar hotuna tare da abokan tafiyar mu, ni kuma baki suna dauka ta hoto, na kati da bidiyo, saboda doguwar riga ta shadda da hula da na sanya. Wasu ma zuwa suke yi su ce don Allah muna so mu dauki hoto da kai, wani ya zo shi kadai wani ya zo da matarsa wani saurayi da budurwa ne suke zuwa.

Nan fa shugaban tafiyar tamu, da yake mutum ne mai barkwanci, Waziri Amadou sai ya ce “To kai Malam Ado ka zama wani gidan tarihi ko gidan zoo, ko kuma gidan kallo ga shi sai baki ne suke ta daukar ka hotuna, to ko kudi za mu sanya ne duk mai son daukar hotonka sai ya biya?” Sai na yi dariya na ce masa “Ka ga kuwa da mun tara kudi, ko da Euro biyar muka ce duk mutum daya zai biya, daga nan zuwa yamma ai da mun tara kudi da yawa” Muka yi dariya mu duka. Na ce “To Danbourgami Magaouata kai za ka zama mai amsar kudi ko?”

Muna cikin wannan magana sai ga wata mata da miji su ma sun zo sun ce “Don Allah za mu dauki hoto da kai” Na ce “To ba komai ku dauka”. Na tsaya matar ta zo ta tsaya kusa da ni mijin ya dauke ta” Sai ni ma na ce “To bari in bayar da kyamarata a dauke mu”. Ta tsaya aka dauke mu tare, suka yi godiya suka tafi, suna fara’a da dariya. A karshe sun ce min daga Barazil suka zo, ni kuma fa, na ce daga Kano, arewacin Nijeriya.

Da muka gama muka dawo, a kan hanyarmu ta komawa masauki dorebanmu Alkabeer ya ce zai kai mu wajen cin abinci na Halal, wato na musulmi. Haka aka yi kuwa. A nan ne na san na ci abinci sosai saboda na sami irin abincin da zuciyata ta yi na’am da shi.
Washegari ranar 12 ga wata muka dawo birnin Paris, in da za mu yi kwana biyu kafin kowa ya koma kasarsa.

Mutanen Nijar jirgin su ya riga namu tashi, bayan karfe bakwai na safe suka taso, ni kuma sai bayan karfe goma sha daya na taso, kuma tafiyar awa biyu ce tsakanin Italiya da Paris, kuma da yake an sami jinkirin jirgi sai bayan sha biyu muka tashi, don haka ba mu iso Paris ba sai bayan karfe biyu na rana. Nan ma a wajen jiran kayana sai da mutane hudu mace biyu namiji biyu suka zo don neman su dauki hoto da ni, wannan karon mutanen Jafan da Cana ne suka zo.

A Paris kuma abin da ya faru gare ni shi ne, na ci wani abinci da ya sa ni atini na wuni a daki, na kasa fita ko’ina sai dai zaman otel, sai da abokan tafiyata suka sayo min magana na sha, sannan na samu ‘yar sa’ida.

Sai washegari ne muka sami damar fita muka zaga gari muka je wajen dugon karfen nan da ake kira Tawa Elfe. Sannan kuma muka je ofishin hukamar da ta shirya wannan tafiya wato OIF, inda muka mika musu rahoton wannan tafiya da muka yi da kuma irin matsayar da muka cim ma da su wadannan kamfani na Arti Grafiche don su ajiye a ma’adanar su ta hukamar OIF.

Wannan tafiya dai ta ba mu wata dama da muka hada huldar yin aiki da wannan kamfani na wallafa kuma mun karu da ilmi mai yawa a wadannan kasashe biyu, sannan kuma a cikin rubutun da nake na littafina na tafiye-tafiye mai suna GANI DA IDO… na dada samun abubuwan da zan sanya a cikinsa kamar yadda na samu a bara lokacin da na je kasar Jamus.

Fatanmu dai Allah ya sa wannan ilmi da muka samu ya zama ya amfanar da jama’armu marubuta da mawallafa da kuma sauran jama’a masu karatu.

Tuesday, March 30, 2010

TAFIYA MABUDIN ILMI: Balaguron Kwanaki 26 a Kasar Birtaniya

Masu iya magana suna cewa, tafiya sannu-sannu kwana nesa, wannan haka yake, ga shi har na yi kwanaki ashirin da shida a kasar Birtaniya, a kan tafiyata don rubutun littafin GANI DA IDO...da kuma nuna fim din SANDAR KIWO.

Filin jirgin saman Amsterdam da Heathrow

Lokacin da muka sauka a filin jirgin saman Amsterdam inda za mu sauka mu hau wani jirgin da zai karasa da mu London, ba mu jima ba muka sauya jirgi muka tashi zuwa filin jirgin Heathrow na London, misalin karfe 7. 40 muka fito muka nufi wajen jami’an kula da shige da fice, aka fara duba fasfot dinmu, sai da suka tambaye ni me na zo yi nan London, na shaida musu ni marubuci ne kuma na zo ne a kan rubutun littafi da nake yi a kan tafiye-tafiye a Afrika da turai, aka kuma nemi a ga tikitina na komawa da kuma kwanakin da zan yi, duk na nuna su, sannan na wuce.

Da na fito wajen da masu zuwa tarbar baki suke, sai na tsaya don in ga wadda ta zo tarba ta wato Katrin Schulze, wata Bajamishiya da take karatun digiri na uku, wato tana neman takardar shaidar dakta a fannin zane-zane. Bayan wasu ‘yan mintina sai ga ta nan ta karaso inda nake, don lokacin da na fito ita kuma tana wani bangaren.

Daga nan muka nufi wajen shiga jirgin kasan karkashin kasa don isa gida. Mun kai minti arba’in muna tafiya kafin mu isa gidan, don gidan yana arewacin London. Gidan yana lamba 46 Park Road, Turnpike Lane, London N15 3HR. Gidan dalibai ne a cikinsa su bakwai, mata uku mazu hudu, daliba daya mai suna Alina Demitron daga Balgeriya, sai Katrin Schulze daga Jamus dayar kuma Caroline dag Finland, su kuma mazan biyu Dr. Abdullahadi Bala Yahaya daga Kano- Nijeriya, da Dr. Isa Jibril jihar Neja-Nijeriya, akwai kuma Khairul Islam da kuma Reza dukkansu daga Bangaladash dukkansu suna karatun digiri na uku ne.

Bayan na dan huta ne muka nufi jami’ar SOAS, don in hadu da manyan shaihunnan malaman Hausa na wannan makaranta, kamar Farfesa Graham Furness da Philips Jigger da sauransu, sannan kuma in ga Dr. Lindiwe Dovey da ke sashen koyar da finafinan Afrika.

Ashe Filashin a nan London batsa ce?

Wani abin dariya da aka yi ranar farko da na sauka a birnin London wajen karfe uku na rana. Mun je na sayi sabon layin waya da zan dinga amfani da shi mai suna lyca sai na ce da wadda ta raka ni wato Katrin, bari in yi miki filashi ki ga lambar tawa, sai ta kece da dariya tana cewa, kai ka yi a hankali wannan kalmar ba mai dadi ce ba a nan garin. Sai na ce kamar yaya? Sai ta ce ai ina ka ce za ka yi filashin kamar ka ce bari in budi jikina ki gani ne.

Sai na ce wani irin jiki? Sai ta ce kamar ka yi tsirara ko kuma makamancin haka, a kan hanyar da mutane suke wucewa ko a cikin mota ko kuma ga wata mace, shi ake nufi da filashin. Na ce to, ai kuwa ba zan kara fadi ba har wani ya ji.

Da muka isa jami’a, mun hadu da mutane da yawa malamai da dalibai wadanda nake sa rai zan gani da kuma wadanda ma ban zata ba, cikinsu akwai Farfesa Ahmad Halliru Amfani na jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sokoto, ya zo yin wasu na labintis harkoki na ilmi na tsawon wata uku, da wani malami daga jami’ar jihar Kano mai suna Ibrahim Abdullahi wanda yake karatun digiri na uku a fannin kididdigar lissafi, dukkanmu mun yi farin cikin haduwa da juna. A wannan rana aka sanar da ni akwai liyafar cin abinci ta maraba da wani Dr. Usman Ladan da ya zo daga jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya, zai yi irin zaman da Farfesa Amfani zai yi na wata uku, za a yi liyafar ranar litinin 01/03/2010 da karfe 12.30 na rana.

Kowace rana mukan zo jami’ar SOAS sannan in kuma muna da tsarin fita ganin gari mu fita tare da Katrin, ko Farfesa Amfani don a nuna min gurare. Duk da yake ana yin ruwan sama jefi jefi, ga kuma sanyi, a haka dai muke fita mu zagaya don in an ce ba za a fita ba don ruwa, to kuwa ba za a yi komai ba kenan, don haka duk da ban saba ba a haka nake fita cikin ruwan.

Wasu daga cikin wuraren da muka ziyarta akwai

London Planetarium da Madame Tussaud da British Museum da Trafalgar Square da Natural History Museum da Buckingham Palace da Tottenham court Road da Oxford Street da Middlesex Street da Houses of Parliament da Tower Bridge da London Bridge da Brixton da Alexander palace da kuma Old Street.

Mun ziyarci Sashen Hausa na gidan rediyon BBC

Ranar 25/02/2010, wajen karfe uku na rana muka nufi gidan rediyon BBC ni da Farfesa Ahmad Halliru Amfani, inda aka yi hira da shi a kan harshen Hausa, kuma mun sami haduwa da wasu daga cikin ma’aikatansu kamar Sulaiman Ibrahim Katsina da Suwaiba Ahmad da Muhammad Jamil Yusha’u da Ahmad Abba Abdullahi da Mansur Liman da kuma Aminu Abdulkadir da kuma Jamila Tangaza shugaba sashen. Mun dade a gidan rediyon, har sai da aka yi sallar magariba sannan muka taho makaranta. A lokacin ne Sulaiman Ibrahim ya gayyace mu cin abinci gidansa da ke wajen garin London wato Forest Gate.

Da ranar ta zo muka je muka ci abinci a gidansa, muka yi sallar magariba da isha’i. Na lura da wani abu da ya birge ni sosai a gidan Sulaiman, wato batun addini, gaskiya bai yi sake zaman Turai ya sa ya manta da addini ba, haka nan iyalinsa, duk ya sanya su bisa turbar addini, sannan kuma suna yin Hausa sosai a cikin gidan, sabanin wasu da in sun fita suke mantawa da duk wadannan abubuwa, wato tarbiyya da al’ada da addini da kuma harshensu, don cikin ‘ya’yansa mata har da wadanda suka sauke Alkur’ani a nan birnin London. Abin dai sai son barka.

An nuna fin din Sandar Kiwo

A ranar Talata 2/03/2010 aka nuna fim din Sandar Kiwo ga dalibai da malaman sassa biyu wato masu koyon Hausa da kuma finafina Afrika, har ma da baki daga wajen makarantar. Cikin mutanen da suka halarci wannan wajen kallon fim sun hada da Farfesa Philips Jagger da Farfesa Ahmad Halliru Amfani da Farfesa Miry Las (sananne a fannin tarihi) da Dr. Lindiwe Dovey da Barau na Chedi wato Williams Barry Burgerss tsohon shugaban BBC, yanzu kuma malamiN Hausa a jami’ar SOAS da Dr. Chege Githiora mai koyar da harshen Swahili da Jamila Tangaza shugabar sashen Hausa na BBC da Jamilu Mustapha Chedi, Kano, wanda yake karatun digiri na biyu a kan wani sabon fanni a Nijeriya, mai suna ‘designing and ergonomics’ a jami’ar Coventry sai kuma Ibrahim Abdullahi, Kano da ke Jami’ar London yana yin digiri na uku a fannin kididdigar lissafi.

Kafin a fara nuna fim din sai da Farfesa Philips Jagger ya gabatar da ni da kuma gajeren bayanin abin da fim din ya kunsa, sannan ni kuma na karanta dan gajeren jawabin dalilin yin fim din da kuma abin da ake fata a yi in an gama kallon fim din, duka cikin harshen ingilishi aka yi jawaban.

Bayan an gama kallon fim din Sandar Kiwo na tsawon awa daya da minti talatin da shida sai aka bayar da dama in da masu son cewa wani abu wanda ya danganci gyara ko shawara ko kuma suka. Mutum na farko da ya yi magana shi ne Dr. Chege Githiora wanda ke koyar da harshen Swahili, ya ba da shawarar cewa ya kamata mu masu shirya finafinan Hausa mu dinga sanya fassara da harshen Swahili don ya samu karbuwa ga wasu sassa na duniya masu amfani da wannan harshe, kuma ya ce kofa a bude take gare mu a wajensa don gudanar da wannan aiki.

Jamila Tangaza wadda take shugabancin sashen Hausa na BBC London, cewa ta yi, an yi kokari wajen shirya wannan fim kuma ya kamata a kara wani kokarin wajen taba wasu fannoni na rayuwar Hausawa musamman na karkara.

Sauran abubuwan da mutane suka bayyana su ne, sun ji dadin ganin wannan fim kuma yana da ban tausayi sosai, ga shi kuma labarin ana gane shi da abubuwan da yake kunshi da shi, cikin sauki ba tare da sarkakkiya ba.
Na Ziyarci garin Oxford
Ranar Laraba 3/3/2010 ne na tafi garin Oxford don ganawa da wata mata mai suna Mary Jay, sakatariyar masu shirya gasar Noma Award for publishing in Africa, wadda ake bayar da fan dubu goma #10,000 (na Ingila), kimanin Naira miliyan biyu da rabi kenan kudin Nijeriya, ga wanda duk ya yi na daya. Tsakanin birnin London da garin Oxford tafiyar awa daya da minti arba’in 1.40 ce, a cikin irin doguwar motar nan mai hawa biyu. Kuma kudin motar fan 16 ne, kamar Naira dubu hudu kenan (4,000) kudin Nijeriya. Mun bar birnin London da misalin 11.19 na safe kuma mun isa Oxford bayan karfe daya na rana. Sai dai lokacin da muka yi da farko za mu hadu da ita sai ya zama tana da wani mitin a lokacikin don haka da na isa sai na kira ta, sai ta gaya min in dan yi hakuri ta gama mitin din.

Lokacin da nake zaman jiran ta ne na shiga kantin sayar da kayan shaye-shaye da ciye-ciye da ke Gloucester Green bus station, na ce a ba ni shayi da madara da ‘meat-pea’ wato fanke a hausa ke nan. An ba ni shayi da madara da wani dan karamin fanke, na tambaya nawa kudin, aka ce fan uku da wasu ‘yan sulalla, kudin Nijeriya kusan N1000 kamar Naira dari takwas kenan, na biya, na zo na zauna ina sha ina ganin gari. Na kalli fanke da shayin nan, na ce Allah daya gari bamban, shayi da madara da dan wannan fanken su ne a kan wannan kudin, da a garinmu ne na sayi shayin wannan kudin Naira dari takwas ai da an ga ire-iren hadin da ke cikin sa, kuma komai da komai sai ka gani a tare da shayin. Na yi dariya na ce haka dai kasashen Turai suke da tsadar rayuwa, amma babu kamar Ingila. Don a tafiye-tafiyen da na yi zuwa Italiya da Faransa da Jamus ba su kai tsadar nan ba.

Da na gama ne na tashi na shiga wata ‘yar kasuwa da aka baje kolin kayan abinci da sauran kayan bukatun yau da kullum har da kayan sawa. Bayan na gama da kasuwar sai na kara yin gaba na biyo layi ina ganin yadda garin Oxford yake. Ban jima ban a koma, wajen wannan kantin daman an muka yi za mu hadu.

Ban jima da komawa wannan kantin ba na ji ta kira ni tana tambayar ina ina, na shaida mata. Ba a yi minti biyar ba kuwa ta iso wajen da nake. Ta yi min tayin shan shayi ko kofi, na ce ai na sha shayi yanzu, don haka muka je ta kabo shayi ta zo muka zauna, muka fara tattauna abubuwan da suka kawo ni, sannan ta tambaye ni me na zo yi London, na shaida mata na taho ne a bisa dalilin rubutun wani littafi da nake yi mai suna Gani Da Ido…, da kuma fim dina da aka nuna a jami’ar SOAS. Ta yi murna kwarai da jin wadannan dalilai na zuwana. Sannan kuma muka shiga tattauna batun wallafa littattafai a kasashen Afrika da kuma wani aiki da take yi a African Books collective. Ta ba ni labarin kasashen da ta je a Afrika, ni ma na gaya mata kasashen Afrika da Turai da na ziyarta.

Mun dade muna hira, da muka gama, sai ta ce na san garin Oxford, na ce a’a wannan ne karo na farko, ta ce na shiga gari na ga yadda yake?, na ce a’a. Daga nan ta ce mu zaga in gani, in dauki hotuna tun da rubutu nake yi na sami wanda zan sa a ciki.

Da yake a kasashen Turai tafiya a kasa an mayar da ita dabi’a, sai muka fara dukan sayyada muna zaga gari, ta nuna min tsufaffin jami’o’in garin da kuma wani kantin sayar da littattafai wanda ya fi kowane dadewa a Birtaniya, wato Blackwell, wanda aka kafa a shekarar 1897.

Bayan mun gama zagawa da daukar hotuna sai muka yi bankwana da ita na dawo wajen da zan hawo motar da za ta dawo da ni birnin London. Mota za ta tashi da misalin karfe 4.10 na yamma, lokacin yana cika kuwa motar ta tashi ba tare da kara lokaci ba.
Na bata a birnin London

Mun iso London kusan karfe shida na yamma, lokacin dare ya yi tun da an yi sallar magariba. Ashe zan bata ban sani ba, lokacin da muka isa garin kafin mu karasa tashar da ya kamata direba ya kai mu sai ya yi sanarwa a cikin motar cewa ba zai karasa Burkingham Palace Road ba a nan Victoria zai tsaya, kuma bai shiga cikin tashar da motocin suke tashi ba, a hanya kafin ya karasa ya tsaya, ni kuma waccan tasah na fi ganewa ban gane nan inda zai ajiye ni ba, amma babu yadda zan yi sai na sauka, na je wajen da ake shiga motoci masu zuwa wurare daban-daban, wato wurin tsayawar motoci. Na duba duk taswirar da ke makale a jikin allon sanarwa amma ban ga wajen da zan je ba, wato Russell square, don haka sai na ce to bari in kira mai masaukina ta gaya min yadda zan yi, na kira ba ta dauka ba sai salular ce ta amsa da kanta, na bar mata sako, sai na kira Farfesa Ahmad Halliru Amfani don ya gaya min ta yadda zan yi in koma jami’a, sai ya ce gaskiya bai san wace mota zan hawo ba amma in shiga tashar jirgi in hawo jirgin da zai zo Russell square in da jami’ar take kenan, wato shi ya fi sanin hanyar jirgi fiye da mota. Na sake karasawa can inda tashar take na tambayi wani ma’akiacin wajen, bakar fata ne, ya duba taswira ya ce in yi nan zan ga wajen, da na zo wajen hanyar da zan bi in hau jirgi na dauko katina na sanya a shingen da aka yi a kan hanyar, amma karfen ya ki budewa, don haka na tambayi wani ma’aikacin wajen, sai ya karbi katin nawa ya kara a wani waje sai ya ce sai na zuba kudi a ciki, ga wajen da zan je can in biya a kara min.

Na yi turus, na kadai ina cewa, ni da nake da kudi a ciki yaya za a ce sai na kara kudi bayan kudina ba su kare ba, fan 25 na fara sawa lokacin da na zo, sannan na kara fan 21 gaba daya ina da fan 46, kimanin Naira 11,500 na sanya a katin don hawa mota. Sai na ce gaskiya ba zan kara ba bari in nemi inda mota take in hau.

To fa! Ashe na yi gudun gara na cim ma zago, da na sani ma kara kudin na yi in hau jirgin kawai. Da na tafi a kafa na samu inda zan hau mota amma ba mai zuwa inda za ni kai tsaye ba, sai an sake hawa wata motar, na hau mota ta sauke ni a Holborn, nan ma ba a sauke ni a daidai inda zan gane ba, amma na tambayi matar da take tuka wannan babbar motar, da zan sauka ta yi min wani baubawan kwatance wanda ban gane ba, na yi ta bilinbituwa da buliya a tsakanin wajen, mahadace kamar biyar, na yi ta safa da marwa a wajen ban gane ba, na yi ta kokarin kuma in kira lambobin wayar Katrin ko Farfesa Amfani amma baturina ya mutu, don haka babu sauran gyaran mai kalangu ya fada ruwa, wato dai ba sauran sadarwa tsakanina da masu yi min kwatancen hanya, don haka yanzu sai abin da hali ya yi dan daudu a kiyama. Don haka ya zama wajibi in san yadda zan yi in dawo da kaina makaranta ko ta halin kaka, don haka sai na cire tunanin kiran kowa a waya, na shiga neman mafita.

Na fi minti goma sha biyar ina ta bin wajen tsayawar motoci ina karanta taswira don in ga motar da zan hau. Ina nan ina dubawa sai na ji murya ta bayana an ce, da gani wannan bai san inda za shi ba, na waigo sai na ga Sulaiman Ibrahim Katsina yana murmushi, muka gaisa, na ce kai amma dai Allah ya taimake ni. Na ba shi labarin abin da ya faru, ya yi dariya ya ce ai ka kusa da wajen tsallaka can bangaren ka hau mota mai lamba 73, ita za ta kai ka Russell Square. Muka yi bankwana da murmushi, na tsallaka na hau mota shi ma ya hau mota ya nufi unguwarsu wato Forest Gate.

Ina zuwa makaranta na tarar Katrin ba ta nan ta bazama nema na, amma ta bar sallahu in na zo in jira ta a dakin masu binciki, inda na’urori masu kwakwalwa ne tirmis a ciki da injin juyar takardu ‘photocopy’ da sauran kayan bukatun masu bincike. Na zauna na ci gaba da zaga duniya a cikin yanar gizo.

Bayan na share kusan awa daya ina cikin ofishin tare da wani dalibi dan kasar Bangaladash, sai ga Katrin ta shigo a jigace, ta fi awa biyu tana nemana ba ta same ni ba, ta yi ta kiran wayata a rufe sai murya salular ce take amsa mata. Tana ganina ta yi turus ta dafe kirji ta koma kan kujera ta zauna, tana nuna abin mamaki a fuskarta. Muka shiga tattaunawa kan irin yadda ta damu da kuma rudewa ta rashin gani na da ta yi, har nake tsokanarta ina cewa, ko tana tsoro kada mutanena su ce ta batar da ni a London? Muka yi barkwanci muka gama sannan muka nufi gida.

Na ziyarci yankin Hammers Smith a yammacin London

Ibrahim Abdullahi Kano wanda yake malami ne a jami’ar kimiyya da fasaha ta Kano, yana zaune a gundumar Hammer Smith a yammacin London, unguwar White City da ke Shaferds Bush, kusan shekara uku kenan yake zaune a garin tare da iyalinsa, ya gayyace ni cin abinci a gidandsa. Ranar Alhamis bayan na je BBC an yi hira da ni a filin Taba Kidi Taba Karatu, wajen karfe bakwa na dare ya zo BBC muka tafi tashar jirgin kasa muka je unguwar tasu. A can muka yi sallar magariba da isha’i, sannan muka tsaya muka gaisa da wasu ‘yan Nijeriya, muka dawo gidan muka ci tuwon suman bita miyar kuka da yaji da kuma man shanu. Da muka gama hirar da za mu yi ya rako ne tashar jirgi na dawo Holborn (inda na bata wata rana) na hawo mota na dawo jami’a. Shi ma Ibriahim mutum ne mai riko da addini sosai. A wannan unguwa ta White City gidan talbijin na BBC yake don haka kafin in bar unguwar sai da muka je ginin gidan talbijin din, sannan kuma a wanna unguwa ne babban kantin sayar da kayayyaki da ya fi kowane girma da zamananci a nan London yake, ana kiran sa da suna Westfield. Ibrahim ya nuna min shi, ya ce ba don ba lokaci ba da mun je mun shiga, na ce ba komai tun da ana can ana jira na a jami’a.

Hira da kafafen yada labarai

Tun lokacin da zan taho London na sanar da abokaina da ke kafafen yada labarai na rediyo da jaridu, don haka da na zo nan London sai muka yi ta yin hira da su, ciki kuwa har da sashen Hausa na BBC, su zuwana gidan sau uku. Sannan Rediyo Faransa su ma wakilinsu na nan London Idris Muhammad Aminu, ya same ne har masaukina muka yi hira da shi. Su kuma gidan rediyoyin Kasar Nijar, wato Sarauniya da ke Maradi sau biyu muna yin hira da su kai tsaye tare da Laminu Gwanda, haka nan gidan rediyon Altanative da ke Yamai, mun yi hira shi ma ta kai tsaye da Sule Maje Rejeto. Rediyo Freedom ma mun yi za mu tattauna da Baharu mai gabatar da filin Finafinan Hausa amma matsalar layin waya ya hana mu samu damar yin hirar.

Sai kuma wani gidan talbijin mai suna Success TV, ta wani dan Nijeriya, wadanda suke gudanar da shirye-shirye a cikin harshen Hausa da Turanci, mun yi za a yi wata tattaunawa da ni amma saboda lokacin da za a yi hirar ni kuma na bar birnin London, na taho garin Telford, don haka hirar ba ta yiwu ba.

Na yi kwanaki goma a cikin birnin London, sannan yanzu kuma na kara gaba zuwa ina garin Telford.

Garin Telford

Garin Telford shi ne zangona na biyu a wannan tafiya, kuma a nan garin na yi kwanaki goma sha biyar, sannan na dawo gida Kano-Nijeria, wato ranar Asabar 20/03/2010.

Garin yana da mutane 125,000 a cikinsa, muna iya kiransa karkara, yana kusa da garin Birmingham, gari ne mai yawan ma’aikatu, shi ne garin da aka fara kafa masana’anta a Birtaniya don haka ma suke yi masa kirari da Birth place of industry. Ba mutane da yawa, don haka ma ba za ka dinga ji ko ganin zirga-zirgar mutane kamar birnin London ko Birmingham ko Oxford ko Coventry ko kuma Sheffield ba, wato sauran garuruwan da na ziyarta kenan.

Birmingham

Mun je garin Birmingham ranar Talata ni da mai masaukina Umar Dan’asabe Barde a cikin motarsa don ya sayo rago sannan kuma in ga gari. Bayan tafiyar kamar minti ashirin da biyar muka isa Birmingham, muka isa wani kamfanin sayar da yankakkun raguna na mutanen Pakistan, musulmai. Muka sayo daga nan kuma muka dan zaga gari sannan muka dawo gida Telford.

Garin Coventry

Ranar Juma’a na hau jirgin kasa daga garin Telford na kai ziyarci garin Coventry don in gani da idona, wajen wanda na je kuwa shi ne Jamilu Mustapha Chedi, wanda yake karatun digiri na biyu a jami’ar Coventry. Tafiyar kusan awa da ya ce ta kai ni garin. Da yake mun yi alkawari zai zo tarba ta, ina sauka kuwa na gan shi a tsaye yana jira na, na tarar da shi tare da wani abokinsa mai suna Nasiru Garba Anka wanda yake karatun digiri na uku, wato zai zama dakta kenan a fannin tsara birane.

Haka dai muka tako a kafa mu uku, muna tafiya muna labarin duniya, har muka isa makaranta, Nasiru ya tsaya a makaranta, ni da Jamilu muka isa gidan da yake muka yi alwala muka fito muka nufi masallaci don sallar juma’a. Wajen da ake yin sallar filin wasan kwallon hannu da na Kwando ne, in kuma a daidai lokacin sallar juma’ar akwai wani wasa da za a yi a wajen sai dai masu sallar juma’ar su nemi wani wajen su yi sallar. Yau dai an yi sa’a ba wani wasa da ya zo daidai da sallar juma’a don haka a nan muka yi salla.

Da aka idar da salla muka fito waje muka hadu da wasu ‘yan’uwa ‘yan Nijeriya daya daga Kano, Bashir da Adamu Gwani Yola, daga Katsina kuma akwai Yakubu da Abdulaziz, sai Idris Ahmad Adamawa, muka gaisa muka dauki hotuna tare sannan muka yi bankwana da juna. Daga nan muka nufi wasu wurare da muke ganin za mu iya samun damar ziyarta, tun da ba ni da lokaci sosai, tun da a ranar zan kara gaba zuwa wani garin. Mun je gidan abinci na Nando’s inda muka ci abincin rana.

Wuraren da muka ziyarta su ne, Transport museum da West Ochord da Coventry Cathedral (wajen da Hetila ya yi waruwan bamabama) da IKEA da Coventry University da City Centre da Lower Precincts da Shoping Centre da Coventry Rail Station da kuma Pool Meadow.

Bayan mun gama ziyarar gari mu uku sai muka hadu da wasu dalibai Abubaka Rabi’u Yola daga Adamawa da kuma Binta Umar daga jihar Kebbi, muka zama mu biyar kenan, muka zo tashar mota na sayi tikitin tafiya garin Sheffield inda zan ziyarci Muhammad Jamil Yusha’u na gidan rediyon BBC Hausa. Mun dade muna hira a wajen jiran mota, don sai bayan karfe shida motar za ta tashi. Tafiyar awa uku da rabi za mu yi kafin mu isa garin.

Da mota ta zo muka yi bankwana na shiga mota. Kafin motar ta tashi na kira Jamilu Yusha’u na sanar da shi ga motarmu nan za ta taso yanzu. Ya ce da na zo in kira shi sai ya zo tasha ya tare ni.

Garin Sheffield

Bayan awa uku da rabi muka isa garin Sheffield, muka sauka a tashar mota ta Sheffield Interchange. Na kira na sanar da Jamil. Bayan wasu ’yan mintuna ya zo muka tafi gidansa. A lokacin da muka isa gida wani makocinsa mai suna Dr. Kabiru Abdul Katsina, ya kawo min abinci. Sannan mun hadu da Dr. Sani Damban, wanda yake daga jihar Bauchi.

Washegari da muka fito daga gida mun fara da Royal Hallanshire Hospital inda muka duba matar Jamilu inda take kwance ba ta da lafiya. Daga nan muka je masallaci (Muslim welfare house) muka yi sallar azahar da la’asar, sannan muka je dakin Dr. Bichi wani malami daga jami’a kimiyya da fasaha ta Kano, inda muka dan yi hira, kafin mu fita daga dakin wani malamin ya shigo shi kuma daga unguwar Chiranchi ta cikin birnin Kano yake. Sannan muka fita tare, muka je cikin Sheffield University inda muka je wasu bangarori kamar Firth Court da Information commons (library) da kuma Sheffield museum. Daga nan muka yi bankwana da mutane biyun, ni da Jamilu muka ci gaba muka karasa inda muka shiga jirgin kasa wanda ake cewa Tram muka nufi wata babbar kasuwa da ake takama da ita a wannan gari na Sheffield wato Meadowhall shopping centre da ke South Yorkshire. Sai dare muka dawo gida.

Washegari ranar Lahadi 14/03/2010, Muhammad Jamilu ya rako ni tashar mota, muka yi bankwana ya tafi. Motarmu ta tashi da karfe takwas da rabi na safe. Za mu yi tafiyar kusan awa hudu kafin mu iso birnin London.

Na Dawo Birnin London

Da muka iso tashar mota ta Victoria Coach Station da ke birnin London. Daga nan na shiga underground train wato jirgin karkashin kasa ya kawo ni Finsbury Park daga nan na hau wani jirgin ya kawo ni Turnpike lane, wato tashar jirgin da ke kusa da unguwar da na sauka a London kenan. Daga nan na taka da kafa na karasa gida a 46 Park Road, na iske Dr. Hadi Bala Yahaya a gida tun da yau Lahadi ba makaranta.

Abin da ya sa na dawo birnin London don mun yi magana da Minista wato mai gidan talbijin da rediyo na Success, za su yi hira da ni, kuma mun yi alkawari da su ranar litinin da karfe goma sha daya da rabi na safe zan je wajensu.

Washegari na tafi tashar jirgin kasa na hau jirgi daga Turnpike park na sauka a Finsbury park, amma da yake ban taba zuwa Seven sisters train station ba sai na tambayi wani bakar fata mai aiki a wannan waje, sai ya nuna min inda zan hau jirgin da zai kai ne can wajen da zan je. Muna ta tafiya sai na ga muna komawa baya, don gas hi mun wuce Finsbury mun wuce Hightbury Islington, wato wasu tashoshi da na wuce a kan hanyar da na baro gida, sai na natsu na kalli taswirar da take nuna hanyoyin da jirgin yake bi, kawai sai na ga ashe kwatancen nan ba daidai mutumin ya yi min ba, wato kamar ni gabas zan yi shi kuma ya sa na hau jirgin da ya yi yamma, wato hanyar da na baro, don haka ana zuwa babbar tashar jirgin kasa ta Kings Cross St. Pancras sai na sauka na koma bangaren da jirgi zai kai ni inda zan je, ana zuwa Finsbury na sauka na sauya wani jirgin ya kai ni Seven Sisters.

Ni kadai ina dariya a zuciyata ina kuma cewa, amma dai wannan mutumin takadari ne, yaya zai yi min kwatancen banza yana nema ya sake batar da ni kamar yadda ya faru gare ni a ranar Laraba 3/3/2010 lokacin da na dawo daga garin Oxford?

Da na isa Seven Sisters train station sai na kira shugaban gidan talbijin din cewa ga ni na iso, ya kwatanta min inda ofishinsu yake, na karasa ofishin.

Mun dade muna hirar gida Nijeriya tun da shi mutumin Kaltungo ne ta jihar Bauchi. Daga baya ne muka yi hirar a talbijin ta wajen minti talatin. Bayan mun gama kuma mun dade muna tattauna wasu batutuwa, sannan muka taho tare da shi a cikin jirgin kasa zuwa jami’ar SOAS, inda za mu hadu da Farfesa Ahmad Halliru Amfani a wani kantin sayar da littattafai mai suna Woter storn. Muka shiga cikin kantin muka same shi muka zagaya cikin kantin muka duba littattafai ya sayi wadanda zai saya. Daga nan muka taho zuwa tashar jirgi ta Kings Cross St. Pancras, muka yi bankwana da Farfesa Amfani ya koma, mu kuma muka tafi gida, amma mun rabu a hanya, shi Minista ya nufi unguwarsu ni ma haka.

Na Dawo Garin Telford

Washegari na sake hawa mota da misalin karfe daya na rana na nufi garin Telford, kuma za mu yi tafiyar awa hudu da minti goma kafin mu isa garin. Da misalin karfe biyar da minti goma muka isa.

Ranar juma’a 19/03/2010 ne muka je wajen gadar da aka fara ginawa a kasar Birtaniya, wato Iron bridge da ke garin Telford, gadar ba wata babba ce ba, haka kuma matsallakar ruwan ita ma ba mai girman gaske ce ba. An gina gadar a shekarar mdcclxxix 1796. Sannan kuma mun zagaya wurare da dama har da wajen ma’adanar sinadarin nokilaya na da da kenan garin Telford.

Na Baro Birmingham

Washegari da safe bayan karfe hudu na safe muka shiga motar Umar Dan’asabe, mai masaukina muka nufi garin Birmingham don ya kai ni filin jirgin sama, inda zan hau jirgin da zai kai ni Amsterdem. Mun isa filin jirgin wajen karfe biyar na safe.

Bayan an auna jukunkunana guda biyu, an sanya musu alama mai dauke da sunana, aka aika da su wajen jirgi, muka fito waje ina rataye da jakar kwamfutata da kuma wata karamar jakar a hannuna, muka yi bankwana da Dan’asabe, ya hau motarsa ya tafi ni kuma na koma cikin filin jirgi, na hau saman bene inda zan jira lokacin tashin jirgina, wato karfe 7.45 kenan. Na bi layin da jami’an kula da shige da fice da kuma sauran jami’an tsaro suke duba mutane, aka caje mu aka ba mu damar shiga inda za mu jira jirgi.

Lokaci na cika muka shiga layin shiga jirgi da kuma duba tikitinmu don shiga jirgi. Bayan mun shiga direban jirgi ya ba mu hakuri cewa zai yi dan jinkira na mintina goma sha biyar saboda ana jiran ruwan sha da za tafi da shi a cikin jirgin don bukatar fasinjoji. Tafiya tsakanin Birmingham zuwa Amsterdem za ta dauke mu awa biyu da minti goma sha biyar.

Filin jirgin Amsterdem

Mun sauka da misalin karfe goma na safe, sannan kuma za mu jira wani jirgin da zai tashi da misalin karfe daya da minti hamsin.

A zaman jiran da za mu yi ne muka hadu da mutane daban-daban wadanda za su zo Kano wasu kuma Abuja, muka yi sallar azahar da la’asar tare da wasu daga cikinsu kafin lokacin tashin mu ya yi. Lokaci yana yi muka shiga layin da za a caje mu da kayanmu na hannu. Sanna muka shiga jirgi muka taso da misalin karfe daya da minti hamsin.

Mun iso Abuja da misalin karfe takwas saura minti biyar. Masu sauka Abuja suka fara sauka, sannan aka ce mu ma mu sauka mu jira zuwa wani lokaci kafin mu koma cikin jirgin a karaso da mu Kano, mutanen da za su zo Kano sun fi ashirin. Da sauka wasu daga cikinmu suka yi sallar magariba da isha’i, muka ci gaba da jira.

Hazo ya Hana mu Sauka a Kano

Bayan kamar minti talatin da saukarmu a Abuja sai ma’aikatan jirgin KLM suka zo da wata sanarwa, suka ce duk wadanda za su je Kano su matso gaba za su yi mana wani bayani. Muka matso muka bude na zomaye (kunnuwa) muka kuma zura musa na mujiya (ido) don mu gani kuma mu ji mai za a ce.

Sun bayyana mana cewa jirgin su ba zai iya zuwa Kano ya sauka ba saboda babu kyan yanayi, don haka sai dai mu yi hakuri su kai mu otel din Shareton mu kwana zuwa gobe su gani in yanayi ya yi kyau su sa mu a jirgi in babu kuma kyan yanayi su sa mu a mota su kai mu Kano. Don haka ma tuni sun fito mana da kayanmu na hannu da ke cikin jirgi sun ajiye a kan hanyar tafiya shiga jirgi, don haka kowa sai ya je ya dauko jakunkunansa, amma fa da gunaguni, cewa don mai za su fito mana da kaya ba za su bari mu je mu dauko da kanmu ba? Idan wani abu ya bata a kayanmu fa? Haka dai muka fito wajen daukar manyan jakunkunanmu muka dauko su niki-niki, muka fita waje muka loda su a kan motocin da aka tanada don kai mu otal. Ba mu isa otal ba sai bayan karfe goma na dare, kowa aka ba shi daki. Ni a hawa na bakwai aka sauke ne a daki mai lamba 740.

Washegari da safe wajen karfe takwas aka bugo min waya a dakina aka sanar da ni cewa ana so nan da minti goma in sauko za a dauke mu a mota zuwa Kano.

Da muka sauko muka ga katuwar motar nan wadda ake kira Makfolo, mai daukar mutane kusan saba’in. Mutanen da suka hau motar ba su kai mutum ashirin ba, don wasu tun da safe suka buga sammako, wasu kuma ba su kwana a nan otal din ba sun yi tafiyarsu tun a daren.

Kafin mu taho aka ce da direba filin jirgin Malam Aminu Kano da ke Kano zai kai mu, kada ya sauke kowa a hanya, don su masu jirgin suna so su tabbatar duk wanda suka dauko a motar sun sauke shi a filin jirgin Kano.

Bayan mun taho ne, aka tsaya a gidan mai direba zai kara mai, sai wasu mata guda uku, daya daga kasar Sin wato Cana da kuma biyu daga Amurka, suka ce ai su atabau ba za su ci gaba da tafiya a wannan mota ba sai dai direba ya juya ya mayar da su Abuja, ba zai yiwu ba su yi tafiyar awa biyar a motar da ba ta da na’urar sanyaya mota ba, wato iya kwandishan. Nan fa aka shiga dogon Turanci da wadannan mata, wata da cikin abokan tafiyarmu ta sauko ta ce, gaskiya ba za mu koma Abuja saboda mutum uku ba, sai dai in a nan za ku sauka, amma ku sani cewa nan wajen ba tashar mota ce ba, in so kuke ku sami mota wadda take da tabbacin tsaro sai ku bari mu je tasahar motar Kaduna sai ku sauka ku hawo wata, in kuma kun daukar wa kanku za ku sauka a nan shi kenan. Wata daga cikin matan ta ce su za su kara kudi direba ya sanya musu iya kwandesha. Direba ya ce motarsa fa babu na’urar sanyaya cikinta.

Haka dai muka bata lokaci ana ta sa-in-sa, har dai ni ma na sa baki na ce to ku in mutum ya je garin da ba nasu ba ai yana koyar zama da yanayin da ya tarar, ni da na je kasashen Jamus da Italiya da Faransa da Birtaniya, ai yanayin sanyi na tarar, haka na dinga sanya riguna hudu wando uku, ban ce sai na sami irin yanayin kasa ta ba, saboda haka tun da kun zo lokacin zafi ai sai ku yi hakuri, tun da dai motar da aka ba mu babu na’urar sanyaya cikinta, idan ma akwai mai laifi to kamfanin jirgi na KLM ne, tun da ya san akwai irinku jajayen fata masu son sanye sosai, mu in muka bude taga sanyin ya ishe mu. Don haka kuma sai ku bude tagogin kusa da ku. Sai ta ce, ai tana da cutar asma ba ta son kura da wannan hazon. Nan fa kowa ya ce, to wadannan matan dai ba masalaha suke nema ba, suna so su bata mana lokaci ne kawai, don haka direba ya sauke musu kayan su in ba za su tafi a cikin motar ba. A karshe dai bayan an shafe lokaci mai tsaho ana ja-in-ja suka shiga motar muka tafi, suna bude tagogi isaka ta wadace su, har da mai yin gyangyadi a cikinsu.

Ba mu muka iso filin jirgin saman Malam Aminu Kano ba sai bayan karfe hudu na yamma. Muka sauka aka sauko mana da kayanmu kowa ya shiga motar da ta zo tarbarsa, muka yi bankwana da duk abokan tafiyarmu, har da masu son sanyi a mota.

Kadan daga Darussan da na Koya a Birtaniya


Tsadar Rayuwa

Wani abu da na fahimta akwai tsadar rayuwa a kasar Birtaniya fiye da sauran kasashen Turai da na ziyarta wato Faransa da Italiya da Jamus, saboda harajin abubuwa da yawa da suke hawa kan duk wani wanda yake zaune a kasar yana aiki, bisa dan abin da na fahimta zan bayar da bayani don ba duka na sani ba.

Mafi saukin abinci kamar shinkafa da naman kaza da mutum zai saya a kantin sayar da abinci na Larabawan Pakistan ko Indiya ko Indunusiya shi ne na fam biyar, kamar N1,250 kenan a Nijeriya. Wato a rana daya za ka ci kamar N3,750. Amma in mutum shi zai dafa abinci da kansa ya fi masa saukin kashe kudi a kan ya dinga sayen dafaffae.

Abin hawa kuwa in za ka sayi katin hawa babbar mota (bus) na sati daya za ka biya kamar fam 25 wato N6,250 kenan a Nijeriya, duk inda za ka a cikin London a cikin wannan satin, in sati ya cika kudin sun kare sai ka sake zuba wasu. Idan kuwa tasi za ka hau, wato ta masu kudi kenan, suna duba malejin kirga tafiyar ne, wani lokacin kana iya biyan fam 50, wato kamar N12,500, hawa daya kenan. Babbar mota ce mafi sauki, sai jirgin kasa ke bin ta sai kuma tasi ita ce ta fi su tsada.

Sannan akwai wasu harajai da kowane mazaunin wannan kasa wanda yake da aikin yi a kasar, misalansu su ne: Talbijin da rediyo da ajiye mota a wajen ajiya ko a kofar gidanka da lafiya da rai da mage ko kare (in kana da su) da kayan gida kamar kujeru da gadaje da firinji da suran makamantansu. Haka ma akwai harajin gidan da kake haya bayan kudin hayar gidan da kake biya, akwai takardun mota da za su ba ka damar hawa titi ka yi tuki, sannan duk shekara sai ka kai motarka an duba lafiyarta in da abubuwan da suka mutu a sa ka sauya su in ba ka sauya ba ba kai ba hawa titi da motar. Akwai batun wutar lantarki da gas na dafa abinci da dumama gida da tarho da internet sannan akwai babban harajin da ya fi kowane yawa shi ne na albashin da kake dauka a ma’aikatarku ko makaranta in malamin makaranta ne ko kuma ma’aikacin gwamnata, suna biyan harajin akalla kashe talatin cikin dari 30% na kudin da suka karba duk wata.

Ida muka dubi wadannan abubuwa za mu gane cewa mu muna rayuwa cikin saukin farashi kenan, domin da yan kudi kadan sai ka ci abinci ka koshi, ko da yake ba mu da wadatar wuta da ruwa da tsaro da sauran abubuwan more rayuwa. Haka harkokin ilminmu duk suna da nakasu in muka kwatanta su da na wadannan kasashe da suka ci gaba.

Bayar da ilmi ga ‘yan kasa

A kasar Birtaniya duk dan kasa a ba shi ilmin Firamare da sakandare har da difiloma a kyauta. Idan kuma ka zo shiga jami’a to in iyayenka ba su da karfin daukar nauyin biyan kudin makarantarka, gwamnati za ta ba ka rancen kudin karatun da za ka yi, kudin cin abinci a lokacin karatun kyauta za a ba ka, sai lokacin da ka samo aiki sannan ka fara biyan gwamnati kudin da ta baya maka na makaranta a hanli a hankali.

Jami’o’i

Tsarin koyarwa a jami’o’in Birtaniya yana da ban sha’awa, don akwai duk kayan aikin da ake bukata, kuma ga malamai, sannan ba a tara cunkoson dalibai da yawa a cikin aji daya, kamar yadda a kasashenmu masu tasowa suke yi. Na halarci wani aji da ake koyar da harshen Hausa a jami’ar SOAS, London, dalibai biyar ne kawai, kuma yadda ake koyar da su abin sha’awa da birgewa.

Dalibai masu yin digri na uku kuwa kowane an tanadar masa kwamfuta da zai yi aiki da ita da kuma injin juyar takardu a cikin wani ofishi da aka tanadar musu. Wata jami’a da na ziyarta da ke garin Coventry mutune bakwai ne kacal a ofishin da ke dauke da wadannan kayan aiki. Kuma ‘yan kasahe daban daban, har da dan Nijeriya da ya fito daga jihar Zamfara.

’Yancin Mata da yara
Na kuma fahimci mata da yara kanana ana ba su fifiko fiye da maza, kuma ba za a taba bari namiji ya wahalar da mace ba, haka kuma ba za a taba yarda iyaye su wahalar da yaro ko su takura masa ba, in haka ta faru kuwa aka yi wa iyayen gargadi daya zuwa uku ba su gyara halinsu ba to, za a kwace dan ne daga gare su a bai wa wani ya kula da shi.

Tsofaffi

A tsarin zaman kasar Birtaniya, an wajabta wa duk majiyin karfi in yana tafiya a hanya ya ga dattijo ko dattijiwa ya kauce a bat a hanya, haka in a cikin mota ko jirgin kasa kana zaune a kan kujera ka ga dattawa dole ne ka ba su wajen zama kai ka ta shi ka tsaya

Addini

Ba a damu da batun addini ba a kasashen Turai, in ka fiye maganar addini sai a yi maka wani irin kallo na ka fiye tsattsauran ra’ayi.

Abubuwan suna da yawan gaske, amma zan bar su haka sai a cikin littafin GANI DA IDO… ku ma za ku gani da idonku.