Monday, June 18, 2007

Gwagwarmayar Da Take Gaban Hausa(Wa) A Karni Na 21

Hamisu Isa Sharifai

An Gabatar Da Wannan Takarda a Bikin Makon Hausa Na Kungiyar Habaka Hausa, Ta Daliban Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Da Afrika, Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, a Dakin Taro Na Abdullahi Smith, Samaru – Zariya. Ranar 21 Ga Yuni, 1997



- Mai girma shugaban wannan zama, Shaihun Malami Dalhatu Muhammad
- Mai girma Uban Biki, Mallam Adamu Ibrahim Malumfashi
- Mai girma shugaban karamar hukumar Zariya, Alhaji Isma’ila Nabara
- Wakilin mukaddashin shugaban jami’a, Shaihun Malami Abdullahi Mahadi
- Shugaba da wakilan majilasar kungiyar habaka harshen Hausa
- Manyan baki maza da mata

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala wa Barakatuhu.

Ina mai matukar farin ciki da jin dadi saboda wannan girmamawa da aka yi mani, aka gayyato ni don yin jawabi a wannan wuri, indo Kungiyar Habaka Harshen Hausa ta ke bikin makon Hausa, na wannan shekara, a nan Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. Wannan take da aka ba ni in yi magana a kansa babba ne. Sannan kuma wurin da zan yi maganar, a gaban shugabannin sashen harsunan Nijeriya na Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya, shi ma hamshaki ne, saboda haka abin yana da ban tsoro. To, amma abin ya zo mani da sauki domin wannan sashe na harsunan Nijeriya gida ne a wuriña. A lokacin da nake Babban Editan Mujallar Rana wannan sashe ya taimaka kwarai da gaske. Lokacin da muka fara buga Mujallar Rana sai ya kasance ana samun matsaloli a kan adabi da nahawu. Da taimakon Malamai daga wannan sashe muka samu muka yi maganin wannan lalura.

Wadannan kuwa sun hada da su Mallam Bello Al-Hassan, (wanda a karshe shi ya karbe ni a zaman Babban Editan Mujallar Rana), Mallam Abubakar Kafin Hausa, da kuma shugaban sashen a lokacin, wato shugaban wannan zama, Shaihun Malami Dalhatu Muhammad. Saboda haka ba ni da fargaba; a gaban yayye da kanne nake, idon na yi kuskure to dama aikin naku ne, sai ku gyara.

Harshe: Gwagwarmayar da take gaban Hausa(wa) a karni na 21, magana ce ta harshe, kuma ta shafi sauran harsuna. Saboda hake dole mu fara ta kan nasabar da take tsakanin harsunan da kuma tushensu. Kamar yadda wani masanin harsuna, Shaihun Malami T. Hodge ya ce, a wajen taron kara wa juna ilimi kan harshe da adabin Hausa a Jami’ar Bayaro ta Kano, ranar 7-10 ga watan Yuli, 1978; dukkan harsuna sun tsiro daga tushe daya ne- Lislak. Daga wannan an sami manyan rassa guda biyu wato “Afroasiatic/Homito-sometic da Indo-European/lndo-Hitite”, su kuma suka haifar da wadansu rassan har zuwa harsunan da muke amfani da su a yau.

Misali; harshen Hausa ya tsiro ne daga reshen Afroasiatic wanda ya kunshi manyan rassa kamar haka: Afroasiatic/Hamawa da Samawa
Semitic – Larabawa da Yahudawa
Egyptian - Misirawa
Berber - Buzaya -
Cushitic - Samaliyawa da Galinyawa
Chadic - Hausawa

Wannan ya nuna mana a fili nasabar Hausa da harsunan gabas ta tsakiya da Arewacin Afrika. Haka kuma a nan kusa ma akwai harsuna da dama wadanda su kuma rassa ne da suka tsiro daga jikin Hausa, wato ke nan, shi harshe ba kirkirarsa ake yi ba. Canji ne yakan faru a harshen farko, wanda ake amfani da shi, kuma dalilai da dama na iya kawo wannan canji, ciki har da al’ada da addini da siyasa da tattalin arziki.

A yanzu haka akwai harsuna kusan dubu biyar (5000) (Shaihun Malami Joseph H. Greenberg) da ake amfani da su a duniya. Daga cikin wannan adadi; kadan ne za su kai karshen wannan karni - duk sauran za su mace - wato a daina amfani da su. Harsuna da yawa sun mutu a tarihi, yayin da wasu suka sami damar yin tashin gwauron zabo. Misali, masu amfani da harshen Turanci a farkon karni na goma sha tara 19 (kusan shekaru 200 da suka wuce) ba su fi mutun miliyan 15 (goma sha biyar) ba (Margaret M. Bryant) amma a yau, akwai sama da mutun miliyan 400’ (miliyan dari hudu), masu amfani da harshen Turanci. Game da harsunan da suka mace kuwa, sai dai mu ce Allah ya jikansu; amma yaya za mu yi mu raya namu? A nan sai mu fara duba ainihin harshen Hausa daga farkonsa zuwa yanzu.

Hausa: Harshen Hausa da al’adun Hausawa sun dade a wannan nahiya tamu. Amma harshen ya samu bunkasa ne a karni na goma (10) a lokacin da daulolin kasar Hausa suka kafu kuma suka samu ci gaba, Labarin wayawar kasar Hàusa ya yadu zuwa daulolin da ke kusa irin su Gana da Mali da Borno. Daga nan aki fara samun masu kasuwanci suna zuwa kasar Hausa. Da haka labarin kasar Hausa ya shahara har masu kasuwanci daga kasashen Larabawa da sauran kasashen gabas suka dimanci kasuwannin kasar Hausa. Tare da wannan kasuwanci Musulunci ya shigo kasar Hausa a karni nas 13-14 (kusan shekaru dari bakwai da suka wuce)

Zuwan Musulunci aka fare ilimin arabiyya wanda shi ya haifar da rubutun ajami. Kafin wannan lokaci ba wata shaida da ta nuna yin amfani da wani tsari na rubutu a al’ummar Hausawa. Shehu Usman Danfodiya da almajiransa sun yi amfani da shi sosai wajen jaddada ilimin addini. Rubutun ajami da shi aka yi ta amfani har lokacin da Turawa suka zo, a farkon karni na 20 (kusan shekaru 100 da suk wuce). Da Turawa suka zo, sai suka gina rubutun rumawa (boko) a kan na ajami. Haka aka ci gaba da koyar da karatu da rubutu a cikin Hausa. (Abubakar Imam).

A shekarar 1930, gwamnati ta fara buga jarida ta Hausa, Jaridar Nijeriya ta Arewa. Sannan kuma gwamnati ta kafa ofishin fassara a Zariya, a karkashin wani Bature, Mr. Tailor. Aikin wannan ofishi shi ne fassara da wallafa littattafai wadanda aká juya daga wadansu harsuna zuwa Hausa. Bayan Mr. Tailor, sai R. M. East ya zo ya ci gaba da aikin. A lokacin ne Mr. East da Abubakar Imam da abokan aikinsu, suka kafa harsashin rubutun Hausa sosai; suka kuma daidaita mata ka’idaji. (Abubakar Imam). Gasar talifi, wadda aka shirya a shekarar 1934 ta bunkasa boko sosai. A sakamakon gasar ne aka sami shahararrun littattafan Hausa irin su:
1. Shaihu Umar na Abubakar Tafawa Balewa
2. Ruwan Bagaja na Abubakar Imam
3. Jiki Magayi na Mr. East da M. Tafida
4. Idan Matambaya na Muhammadu Gwarzo
5. Gondaki na Mallam Bello Kagara

Bayan wannan gasa ce, Mallam Abubakar Imam ya kama aiki a ofishin fassara, inda ya rubuta littattafan Magana Jari Ce, juzu’i na 1-3 da Karamin Sani juzu’i biyu da kuma Ikon Allah wanda shi da abokin aikinsa, R. M. East suka wallafa.

A cikin watan Janairu a shekarar 1939, sai aka fara buga Gaskiya Ta Fi Kwabo, wadda ita ce jaridar farko da aka rubuta da Hausa zalla, (Jaridar Nijeriya Ta Arewa ana buga ta ne gefe guda da Hausa gefe guda kuma da Larobci). Haka dai aka yi ta tafiya, Hausa ta zama harshen karatu a makarantu a koina o arewo hor da kudqncin kasar nan. Sannan to ma shigo wadansu kasashe a nan yammacin Afrika (Imam). Wannan saurin yaduwa da bunkasa na harshen Hausa ya firgita Turawa, saboda haka aka shiga yi mata zagon kasa. Don a hana jihar arewa magana da murya daya, sai aka rika zuga kassashen Hausa da cewa Hausar da ake buga jaridar ‘Gaskiya Ta Fi Kwabo’ ba Hausa ba ce, sunanta ‘Istanci’ ko ‘Gaskiyanci’ Daga nan sai kowane lardi ya fara buga jaridarsa kamar haka:

1. Lardin Sakkwato - Zaruma
2. Lardin Bauchi - Zumunta
3. Lardin Zazzau - Bazazzaga
4. Lardin Kano - Sodangi
5. Lardin Borno - Albishir
6. Lardin Adamawa - Ardo (Fillanci)
7. Lardin Kasar Kuzo - Gamzaki
8. Lardin Binuwai - Nwanga (Tiv)
9. Lardin Katsina - Himma
10. Lardin Ilori - Durosi Otto (Yarbanci)
11. Lardin Neja - Nnanintsu (Nupe)

Daga nan sai aka kawo wani Bature ya bude ofishin koyar da harsuna, mai suna NORLA (Ofishin Adabi na Jihar Arewa). Aikin ofishin shi ne ya wallafa littattafai a cikin kowanne harshe na Arewa. Da yin haka, aiki sai ya tsaya cik, kamar yadda Abubakar Imam ya ce, “Shi ke nan babu sauran’ ken- ken- ken, mai kalangu ya fada rijiya”. Wannan shi ne dunkulallen tarihin harshen Hausa na wannan zamani namu.

Nasabar Harshe Da Ci Gaban Al’umma
Shaihun Malami Joseph Hell, wani Bajamushe masanin tarihi, ya ce “Daukacin tarihi na kowace al’umma labari ne na irin bukace-bukacen da suke da su, da kuma kokorin da suka yi wajen biyan wadannan bukatu.” Wato ke nan daga tarihin Hausa za mu gane irin ci gaban da Hausawa suka samu da kuma irin gwagwarmayar da take gabansu don karo ci gaba a karni mai zuwa - karni na 21 (ashirin da daya)

Tarihin Hausa da Hausawa daga karni na 10 (goma) yana da sauki gwargwado. Amma daga karni na goma zuwa baya yana da malsaloli iri-iri. Wadannan kuwa sun hada har da rashin hanyayin rubutu a lokacin, wanda ya sa ba a sami i sahihiyar hanyar ajiya tarihi ba. Kusan duk abin da aka samu daga lokacin ta hanyar tarihin boko aka same shi, wadda tattare take da gurbace-gurbace, na kara da ragi, daga karni zuwa karni. To amma duk da haka, irin wannan tarihin ya ba mu damar sanin wadansu dunkulallun bayanai na matakan ci gaba da aka samu al’ummar Hausawa na wannan lokaci. Misali, tarihin Daura da Sarauniya Daurama (kafuwar Hausa bakwai). Ko da yake wannan tarihi ya kawo tambayayi masu yawa, kusan fiya da amsoshin da ya zo da su, amma duk da haka ya nuna mana yadda al’ummar Hausa ta riga ta sami wayawar tsarin zaman jama’a da shahararriyar daula, wadda har Bayazid daga kasashen gabas ta tsakiya, ya ziyarta. Haka kuma a Kano, tarihin Barbushe da Tsimbirbira da su da jama’arsu da gina fadar farko a nan Madabo (A. Dakoji) da ginin Fadala ta farko da ta biyu da sauran kare-kare na daga baya da kafuwar sana’o’i kamar Noma da Kira da Rini da Gine-gine da kuma kasuwanci (Barkindo, Bawuro). Duk wadannan shaidu ne na ci gaba da Hausawa suka samarwa kansu a daukacin kasar Hausa, kamar yadda Girkawa da Rumawa da Larabawa, a nasu sassan su ma suka samu.

Zuwan Turawa Da Tauya Ci Gaban Harshe Da Al’adunmu
To amma kusan tun daga lokacin da Turawa suka zo irin ci goban da harshenmu da al’adunmu suke yi sun tsaya cak. Kusan duk wani abu na ilimi ko da koyar da Hausar ne, sai dai a yi da Turanci. Duk wata sabuwar hikima saa dai ka ji ta a harshen Turanci. Harshenmu an mai da shi na hira da wasan yara. Sababbin bincike-bincike na kimiyya da sana’a wadanda wannan zamani ya shahara a kansu, mu ba mu da su sai dai mu koya su a bakon harshe. Tun farkon zuwan Turawa, kokarin da aka yi ta yi shi ne, kafa Turanci cikin harkokinmu, yadda duk yadda muka yi, ba za mu yi tasiri ba, sai ta hanyar harshen Turanci da al’adun Turawa. Wannan kuwa an shirya ne don an san ba wata hanya da za’a ci gaba da bautar da mu sai ta hanyar sabauta harshe da al’adurmu.

Saboda hake sai aka shirya hanya mai sauki wajen samun wannan biyan bukata wato ta tsarin ilimi. Duk wani kokari na ci gaba ya dogara ne da samar da kwakkwara kuma sahihiyar hanyar bayar da ilimi. Wannan kuwa ya hada da tsarin manhaja da harshen koyarwa a makarantu. Lokacin da Turawa suka zo sun tarar da mu da tsarin karatu da rubutu wanda ya riga ya kafu a cikin al’ummarmu. Akwai makarantun alla a ko’ina a kasar Hausa da ake koyar da yara da samari, sannan kuma akwai manyan makarantu na littattafai don ilimi mai zurfi. Har ila yau akwai wurare da dama na koyan sana’o’i daban -daban. Sannan a duk makarantun ana koyan karatun ne da harshen Hausa. Kuma har zuwa yau za ka ga irin wadannan makaratun a ko’ina a kasar Hausa. Wadannan makarantu su suka haifar wa da Hausa hanyar rubutunta na farko wato ‘Ajami’. Sannan kuma ta hanyar wadannan makarantu ne aka sami shugabanni da manyan ma’aikatan hukuma da alkalai da shahararrun malamai wadanda suka samar wa harshen Hausa nahawu da sauran sharuddan karatu da rubutunsa. Wannan babban aiki ya sa harshen Hausa shi kadai yake da salon rubutu nasa na kansa a cikin jerin harsuna na iyalin chadi (cambridge encyclopedia of language).

Farkon zuwan Turawa, wanda duk zai zo sai ya koyi harshen Hausa kafin y iso mana nan. Haka kuma su ma Turawan mulkin mallaka, duk wanda za’a kawo shi aiki a arewacin kasar nan ma sai ya koyi harshen ta yadda jama’a za su iya hulda da shi. Saboda haka da farko ma duk wani aiki da kuma wasu takardu na gwamnati da Hausa ake rubuta su, kuma da Ajami. Don dama haka suka tarar ana yi. A hankali aka fara rubutawa a gwame (Ajemi da boko). Daga baya sai aka daina rubuta ajamin, da tafiya ta yi nisa sai aka daina Hausar ma dungurungun, mukk koma yin komai da Turanci. llar wannan kama karya da ak yi wa harshenmu da al’adunmu shi ne, mu mun zauna ke nan da kayan aro. Tun daga makaranta, yaro ya zo karatu an nuna masa cewa harshensa na iyaya da kakanni, harshen jahilai ne saboda haka ba shi da amfani a makaranta. Harshen Turanci shi ne kawai za’a ya amani da shi wajen ilimi da bincike-bincike da neman abinci da ci gaban al’umma.

To, tun da ba yadda zai yi, sai ya koyi wannan bakon harshe. Wajen koyar harshen kuma, dole a koyi al’adu da dabi’u. Wato ke nan, duk wani mai son ya yi nasarar samun ilimi a wadannan makarantu dole ya zage ya koyi harshen Turanci soai, wajen yin haka kuma dole ya dauki al’adunsu da dabi’unsu. Ka ga, ke nan, idan aka yi sa’a ya kammala karatunsa ya kware, to shi ke nan an samu bakin Bature, kamar yadda mutanenmu sukan kira fitaffun yan boko. Shi ke nan an rasa wannan mutum, damin an riga an jirkita hanyar tunaninsa ta yadda in ba tunanin da Bature ya tsara ba, ba ya ganin komai da daraja. Inda abin ya yi zurfi, za ka ga irin wadannan mutane sun zama ba sa ko iya zama cikin al’ummarsu, ballantana su iya taimaka mata. Sai dai su zama shugabanni ta yadda za su hau kan jama’a da sunan jagora, bayan su kansu ba sa san inda hanyar da suke kai za ta kai su ba. Haka kuma wannan ita ta haifar mana da shugabanni masu sha’awa da kwaikwayon Turawa, har ta sa suka sace kudin jama’a su boya a turai.

Da yawa ba a gane nasabar lalacewar shugabanci da jirkitaccen tsarin ilimi da koma bayan harshenmu da al’adurmu ba. Mutum yana yi maka shugabanci; amma ya dauko harshe da al’ada ta wadansu ya lakaba maka. Kuma yana amfani da su wajen yi maka kama-karya da danniya da yaudara da cim amana. Irin wannan ta’asa ba za ta yiwu ba, idan mutane sun san yadda ake gudanar da al’amurra; wato a cikin harshensu da kuma tsarin da suka sani. To, amma shi Bature dama haka ya tsara kusan duk inda suka yi mulkin mallaka a duniya, irin wannan shirin suke yi. Su kafa makaranta su kawo littattafai wadanda suka rubuta, su kawo malamai, su debi ‘yan kasa su mai da su Turawa. Shi ke nan ko da an ce an ba ku mulkin kai ya zama bonono ne, rufin kofa da barawo. Irin wannan ilimi shi ne ya zame mana sarka ya dabaibaya mu muka kasa ci gaba sai ma baya muke yi da mu da harshenmu da al’adunmu. Gwamnatoci daban-daban kowa ya zo da irin nasa kirarin, arnma har yanzu an kasa gane cutar ballantana a samu magani. Wannan irin irin halin da muke ciki ke nan a yau. Yaya za mu kwaci kanmu. Wannan ita ce tambayar da muke dubawa a wannan zama.

Tarihin Ci Gaban Daulolin Da Suka Shude
Yanzu duniya tana ta ci gaba, ga shi mun kawo karshen karni na 20 (ashirin). Mene ne Hausa za ta yi don kasancewa daya daga cikin Harsuna na ci gaba a karni na 21 (ashirin da daya). Kamar yadda Hausawa sukan ce matambayi ba ya bata, sai dai mu ce Allah ya ba mu sa’a amin. Za mu iya samun amsar wannan tambaya idan muka yi nazarin tarihin wayawar duniyarmu ta yau, da kuma tarihin daulolin da suka shude. Misali, wayawar kan wannan lokaci namu, tushensa yana cikin kokorin da Musulmi da Larabawa suka yi na daga bayyanar musulunci a karni na (7 bakwai) zuwa karni na 13 (goma sha uku).

Kamar yadda na rubuta a wata makala da aka buga a mujallar ‘Hotline’ (May 30, 1987), “Ba sai mun bar harshenmu da al’adunmu na gargajiya sannan za mu fara aikin ci gaba ba’. Kamar yadda wani masanin tarihin Larabawa ya rubuta “A sakamakon saduwa da tunanin Larabawa (musulunci), da karin kaimin sake samun tsofaffin hikimomin Girkawa, kwadayin Turawa ya karu game da karance-karance da falsafa, wanda ya kai su ga karuwar ilimi nasu na kashin kansu, mai yawan gaske, wanda make cin amfani a yau. (Hitti). Daga sanin irin wannan tarihi za’a gane cewa, duk wata al’umma da take kwadayin daukaka wayawar kan dan’adam to dole ta zama gulbin karbar ilimin kimiyya da sana’a ta kyautata su da kuma tanadar da su don amfanin jama’a ta gaba. Tsakanin karni na 7 (bakwai) zuwa karni na 13 (goma sha uku) Larabawa (musulmi) sun zama gulbin kimiyya da falsafar Girkawa. Sun fassara kusan dukkan manyan ayyukan Girkawa a kimiyya da falsafa zuwa Larabci, suka kyautafa su suka kuma gabatar da su ga Turawa da wasunsu, wanda shi ne ya haifar da ci gaban wannan zamani na Turawan yamma. A wajen yin wannan aikin Larabawa ba su zubar da harshe da al’adunsu ba. Sun rike su sosoi. Suka kuma yi amfani da su wajen yin wannan gagarumar gudummuwa ga ’Yan Adam.

Cikin fitattun musulmi wadanda suka yi wannan aiki na fassara akwai irin su, Muhammadu lbn Ibrahim Al-fazzri (ca-806) wanda shi ne ya fassara wani littafin ilimin taurari wanda aka samo daga kasar Hindu, kuma wannan mutum shi ya fara zama fitaccen masanin ilimin taurari na musulmi. Bayansa, saa shahararren masanin taurarin nan AI-khawarizimi (ca 850) wanda ya yi amfani da littattafan Al-fazari da na Girkawa wajen kyautata ilimin taurari. Hake kuma Al-fadi Ibn Nawbakht (ca 815) shi kuma ya fassara aikace-aikacen mutanen Pasha a kan taurari, Shaihun masu fassara kuwa, shi ne, Hunayn Ibn Ishaq (ca 873), wanda shi ne Khalifa Al-ma’amun ya nada shugaban makarantarsa ta fassara. Sau da dama masu fassara sukan kware har su ma ta kai su ga bayar da gudummawa wajen kyautata ilimi. Yahaya lbn Masawayh (ca 857) wanda shi ya fassara wa Al-Rashid wadansu aikace-aikace a kan aikin magani, yana daya daga cikin masu irin wannan basira. Ta fuskar hada magunguna uban tafiya shi ne Jabir lbn Hayyan (ca 776) wanda ya rubuta kundin hada magunguna na farko. Haka kuma cikin fitattun marubuta a kan fannin magani wadanda suka biyo bayan masu fassarar farko, har da su, Ali Al-tabari da Al-Razi da Ali Ibn Al-abbasi Al-Majusi.

Shaihun masana, kamar yadda aka yi masa take a lokacin, Abu-Ali AI-Husayyn. Ibn- Sina shi ne wanda ya rubuta littattafai fiya da 200 (dari biyu) a kan falsafa da Addini da aikin magani da hisabi da ilimin taurari da ilimin harshe da kuma sauran sana’o’i. Fitattun littattafan sa da suka fi suna su ne; Kitab al-shifa (littafin warkarwa), wanda kundi ne na falsafa da kuma Qanun fi al-Tebb, ‘The Canon’ kamar yadda Turawa kan kira shi, wanda shi ma babban kundi ne na ilimin aikin lafiya. An fassara wannan littafi zuwa harshen Latin, sannan Turawa sun yi amfani da shi wajen koyar da likitoci har zuwa karni na 17 (goma sha bakwai). A cikin shekaru talatin na karshen karni na 15 (goma sha biyar) an buga wannan littafi sau 15 (goma sha biyar) Shi wannan littafi ya fi kowane dadewa ana amfani da shi a fagen aikin lafiya, a duniya.

A jerin su lbn-Sina akwai manyan malamai kamar su Abu Yusuf, Yakub lbn lshaq Al- Khindi da Muhammad lbn Muhammad lbn-Tarkhan Abu Nasr Al-Farabi wadanda su ma sun yi fice a fagen falsafa da hisabi da magani da siyasa da aikin ido da ilimin taurari da fasalta kida.

Wajen nazarin taurari an yi shaihunan malamai wadanda suka kiyasta yanayin taurari da duniyoyi da bigirensu, irin su Abu Abdullahi Muhammad lbn Ahmad al-biruni (ca 1050), da Umar al-khayya (ca 1124) wanda saboda tsananin sanin taurari da iya hisabi, ya yi gyara a kalandar Rumawa, ta kasance sai bayan shekara dubu biyar (5000) za ta rasa kwana daya a madadin kwana takwas da takan rasa a duk shekara.

Tarihi na nan cike da sunayan masana wadanda suka yi aikace-aikacen da a yau muke cin albarkacinsu. Duk da kokarin dakusar da sunayansu, duniya ba za ta manta da su ba. Ta fuskar ilimin addini akwai irin su Al-Numan Ibn Thabit Abu Hanifa (ca 767) da Malik lbn Anas (ca 795) da Muhammada lbn ldris Al-Shafi’i (ca 820) da Ahmad lbn Hanbali (ca 855). Ta fuskar Hadisi akwai su Muhammad lbn lsma’il Al-Bukhari (ca 870) da Muslim lbn Al-Hajjaj (ca 875) da Abu Dawud (ca 888) lbn Majah (ca 86) da Al-Nasa’i (ca 915) da Al-Tirmidhi (ca 892).

Ba za to yiwu mutum ya lissafa dukkan wadanda suka yi wannan gagarumin aiki ba, amma ban da wadanda muka fada a baya akwai wasu ma kamar su Jabir lbn Hayyan da Al-fargani da Thabil lbn Qurra da Al-Mas’udi da Al-Tabari da Abul wafa da Ali lbn Abbas da Abul-Qasim da lbn Al- Jazzar da lbn Yunus da Al-Karhi da lbn Al-haitham da Ali lbn Isa Al-Ghazzali da Al-Zarqali da lbn Rushd da sauran masana masu yawan gaske. Wadannan mutane sun yi aiki a kan fannoni masu yawa kamar labarin kasa da tarihi da siyasa da addini da hallitar dabbobi da halittar jikin mutum da gine-gine da Hadisi da shari’a da harsuna da shuke-shuke da wakoki da falsafa da labarai da fasalin kida da dai sauran fannonin ilimi.

Tushen Wayawar Kan Turawa Na Wannan Zamani
Bayan kwace birnin Toleda, a lokacin da daular Andalusiya (Spain) to fara kubucewa daga hannun musulmi, limaman kirista karkashin Arch Bishop Raymon, sun bude makarantar fassara inda aka yi ta aikin fassarar har zuwa karni na 13 (goma sha uku). An tara masana masu yawa daga kowane sashe na Turai, wadanda suka yi kusan shekaru dari da hamsin suna wannan aiki. Zuwa karshen karni na 13 (goma sha uku) kusan an fassara dukkan muhimman aikace-aikacen da musulmi suka yi, kuma an watso shi a kowane sashe na Turai. Wannan ta kawo mu yau, inda Turawa suke rike da tutar wayewar kan wannan zamani.

Nadewa
A nan ya kamata mu gane cewa, amfanin nazarin tarihi shi ne al’umma ta san inda ta fito, da inda take, da kuma inda ta dosa game da harkokinta na yau da kullum. Wannan kuwa sun hada da al’adunsu da addininsu da mulkinsu da ilimi da sana’o’i da siyasa da tattalin arziki da alakarsu da sauran jama’a. Sannan kuma a san cewa, muhimmin amfanin tarihi, kamar kowonne irin ilimi, shi ne aiki da shi. Ana nazari ne don a karu ta wajen fahimtar gaskiya da karya, Adalci da zalunci, kwazo da ragwanci, tattali da al’mubazzaranci. Wannan shi ne zai yi mana nuni da inda al’umma ta kai a nata kokarin; kuma shi ne ma’auninta na shahara ko gazawa gwargwadan kwazon da ta yi (Abubakar Dakaji). ldan muka dubi irin ci gaban da yake kewaya da mu a yau, ta fuskar ilimi da kere-kere, mu Hausawa da sauran mutanen nahiyar Afrika muna da jan aiki a gabanmu. Amma idan muka duba tarihi, kuma muka yi aiki da darasin da ya kunsa, to da ikon Allah; ba wani abu da zai gagare mu.

Misali a halin yanzu duk abubuwan taimakon mutum wajen tafiye-tafiye kamar su kekuna da babura da motoci da jiragen kasa da na ruwa da na sama duk ba mu da su. Kusan dukkan wadansu kayayyakin aiki na zamani wato injina da na’urori sai dai mu dogara da wadansu wajen kera su da kuma gyara su. Haka kuma, ba mu iya biya wa kanmu bukatu ta fannonin aikin lafiya da hada magunguna da gine-gine da ilimi da dai sauran bukatu na yau da kullum. Idan aka yi la’akari da wannan sai mu ga duk wani kirari na ci gaba da muke yi, dori-difiri ne, domin a jingine muke jikin wadansu.

Dago misalan da na bayar na farko muna iya gane muhimmancin harshe da al’ada wajen samara wa al’umma wayewar kai da ci gaba. Muddin harshe da al’ada ba ilimi a cikinsu to wadannan mutanen masu su ba yadda za su ci gaba domin dole su dogara da wadansu wajen samun biyan bukatunsu. Gwagwarmayar da take gaban Hausa shi ne a mai da Hausa harshen ilimi da harshen kimiyya da sana’a, ta zama harshen aiki da ci gaba. Wannan aiki ya shafi kowa da kowa. Shugabanni da masu kudi da sauran jama’a kowa zai bayar da irin tasa gudummuwar gwargwadon iko. Haka kuma wannan aiki na masu ilimi ne. Wato ke nan irin aikin sashen harsuna na wannan jami’a, da makamantan ta da kuma Hausawa da masu jin Hausa masana a fannoni daban-daban na ilimi da sana’o’i. Wannan gagarumin aiki ne ba na makaranta daya ko hukuma daya ko mutum daya ba. Ina ganin zai yi kyau a ce akwai kungiyoyi na masana kamar kungiyar masana aikin lafiya da lissafi (hisabi) da hadin magunguna da ilimin taurari da injiniya da siyasa da tattalin arziki, haka dai, a ce a kowane irin fanni a sami kungiyar Hausa wadda za ta yi kokarin habaka wannan ilimi a cikin harshen. Dole mu share wa marigayi Abubakar Imam hawaye mu sake kafa wani ofishin fassarar, a Zariya da sauran wuraren da suka cancanta don ci gaba da aikin wallafe-wallafe, daga inda suka tsaya. Idan har muna son ci gaban a karni mai zuwa, to dole mu zage dantse mu kawar da jahilci daga cikin harshenmu. Yin haka ya zamo wajibi damin ba za ta yiwu a dogara ga gwamnati wajen aiwatar da wannan aiki ba.

Gwamnatin wannan zamani, kamar sauran na bayanta, tun zuwan Turawa, ita ma Baturiya ce. Sabada haka dole mu yi damara mu fara canjin da kanmu, a hankali, har ta kai mu ga canja gwamnatin ita kanta, yadda za ta dace da bukatunmu.

Wannan manufa tawa ba sabuwa ba ce domin masana da dama sun jawo hankalin jama’a a kanta. Sai dai da yake ni na fito ne kururu ba kamar yadda manyan malamai sukan yi ba, wato a sakaye.

Za a fahimci irin wannan ra’ayi idan aka duba makalar Marigayi Waziri Junaidu wadda ya gabatar a lokacin da aka ba shi digirin girmamawa a wannan jami’a. Shaihun Malami Abdullahi Smith, wanda sunansa ne aka sa wa wannan dakin taro don girmamawa, ya yi irin wannan fadakarwa a cikin shahararriyar makalarsa da ya kira “Muhimmancin akidar ilimi ta jihadin Shehu Danfodiyo a wannan zamani”.

Haka ma Shaihun Malami lsma’ila Tsiga, ya yi irin wannan hasashe a makalar da ya gabatar a taron shugabannin makarantun sakandare wanda aka yi a Katsina a 1993, Wannan makala, kari ce a kan irin wadannan kiraye-kiraye, wadanda na san akwai su da dama, da fatan Allah ya sa a amsa kiran. Sannan kuma a yi aiki da shi, Amin.

Alhamdu Lillahi. Wasalamu Alaikum wa Rahmatullahi Ta’ala wa Barakatuhu.

No comments: