Friday, June 15, 2007

SU WA MUKE Yl WA RUBUTU?

Ibrahim Malumfashi, Sashen Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usman Danfodiyo, Sokoto

An gabatar Da wannan Takarda a Taron Shekara-shekara Na Kungiyar Marubuta Ta Kasa Reshen Jihar Kano, a Dakin Taro Na Dakin Karatu Na Murtala Muhammad, Kano, 31 ga Watan Janairu, 2003


1.0 Gabatarwa
Harshe kamar yadda aka sani, shi ne injin din aiwatar da duk wani tunani na kowace irin al’umma. Shi ne ke tafiya da al’adu da adabi da ma duk wani ilimi na rayuwar dan Adam, a ka ne ko kuma a rubuce. Kila wannan dama cc ta sa ake ba harshe muhammanci, ta yadda wadanda ba su da shi sukan kasance nakasassu, wadanda kuma suke amfani da wani abu makamancin sa, ake musu kallon wadanda ba su cika ba a cikin al’umma. A nan ina magana ne kan bebaye ko kuma masu kama da su da kuma masu amfani da hito a matsayin hanyar sadarwa a tsakanin mutane, misali al’ummar Mazatec da ke kasar Mexico, haka wannan yanayi yake ko a cikin rubutaccen harshe. Duk wadanda ke da hanyar rubuta harshensu, an yi musu kallon wadanda suka ci gaba, suka fi sauran al’ummomi na duniya wayewar kai da sanin abin da duniya take ciki. Wannan shi ne fasali na farko da aka fara amfani da shi wajen gane bambancin da ke tsakanin Turawa da bakaken fatar Afirka, dab da za a yi mana mulkin mallaka. Rubutu, ko kuma in ce harshe shi ne ya sanya wa Turawa ji da kai da kuma tokabo, har suke ganin cewa ba wata hujja da bakaken fatar Afirka za su kyamace su dangane da zuwan su nahiyar a madadin ‘yan jari hujjar wancan lokaci. Ba sai an fada ba, harshe a magance da kuma rubuce ya kara gibi tsakanin Turawa da mutanen Afirka, domin kuwa ko da alburusai da bindigogi da suka yi amfani da su wajen cin wannan nahiya, daga cikin rubutaccen harshe aka samo tunanin.

Saboda haka ko da masana irin su Janh (1963) ke bayanin cewa, ai ko da Turawa suka zo Afirka sun iske mu da wayewar kanmu da tunaninmu da kuma ci gaban zamani irin namu. Shi kuma Rodney (1973) ya kara jaddawa ta hanyar cewa ai zuwan Turawan ya dakushe ne a maimakon ya taimaka wajen ciyar da nahiyar Afirka gaba, kuma ko kafin zuwan Turawa akwai wasu al’ummomi da suke da harshensu a rubuce, akwai kuma wadanda ke da hanyar sadarwa ta gargajiya, irin ‘yan ma’abba da kuma kida da ganguna ko makamantan haka, wannan ba ta nuna mana irin yadda tunanin jama’ar ya kasance ba a zahiri. Domin kuwa mulkin mallaka abin da ya mayar da hankali shi ne sanya mutumin Afirka ya dinga tunani da rubutu a cikin harshen da ba nasa ba, a cikin harshen da zai sanya ya dinga ci gaba da mulkinmu ko da kuwa bayan ya nade tabarmarsa da tsawon shekaru.

Wannan shi ne a halin yanzu ke faruwa a yawancin kasashen da ake yi wa lakabi da masu tasowa ko kuma wadanda ba su ci gaba ba, ba wai a nahiyar Afirka kadai ba, har da sassan duniya da makincin mulkin danniya da mallaka ya shiga cikinsu ya yi kaka-gida. Shi ya sa yau kasar Ingila da masu magana da rubutu da harshen Ingilishi a matsayin harshen uwa ba su wuce ka kwana ka kirge su ba, amma kuma masu magana da Ingilishi a duniya sun fi kowa yawa a doron kasa, shi ya sa ma ake wa harshen lakabi da harshen duniya, ni ko na cc ko dai harshen danniya!
Na fadi haka ne saboda sanin irin yadda tunani da Ingilishi da rubutu da Ingilishi yake nakasa kowace al’umma da ta ba wannan abu niuhimmanci. Ba yadda za a yi al’umma ta ginu ta kuma ci gaba ba tare da kare harshenta da kuma rubuce-rubucenta ba, duk irin yadda mutum zai yi ya ciyar da kasarsa gaba ta hanyar amfani da ilimi da ke cikin littafin da ba a harshensa yake ba, zai kasance cikin matsala da kuma kunci, domin zai zamanto mai yaki da tunani iri biyu, na baki da kuma nasa na gida, wannan na daga cikin abubuwan da suka cunkushe harkar iliminmu da kuma halin da ilimin yake ciki a yau. Wannan abu da muke fama da shi yau, shi ne kuma Turawa suka yi fama da shi tsakaninsu da Larabci, a lokacin da Larabcin yake cikin ganiyarsa. Kusan duk wani ilimi na kimiyya ko fasaha ko kuma na ci gaban al’umm a Larabce yake, kuma dole ta sa Turawa suka yi amfani da nakaltar Larabci don cin moriyar ilimin da ke kumshe a cikin littattafan Larabawa da ke mulkin duniya a wancan lokaci. Daga baya ne Turawa suka fahimci cewa ai yawancin ilimin da Larabawa ke takama da shi su ma sun kwaso wasu ne daga littattafan Girkawa, don haka suka yi watsi da na Larabawa suka koma wa na ainihin, ta haka ne mallakar da Larabawa suka yi wa duniya ta subuce ta koma ga Turawa, musamman na Ingila. Wannan ba wani abu ya nuna mana ba sai cewa gadon gida halal ne ga raggo. Ba ta yadda za a kai ga kololuwar ilimi da ci gaba ta amfani da bakon harshe, domin kuwa komai iya nakaltar harshen wasu da ka yi, ba za ka taba zama kamar su ba, kuma za ka kasance ne a kullum kana magana da su bakin, ba mutanen cikin gida ba, domin kuwa kashi 7 cikin 10 na mutanenmu ba su san da wannan bakon harshen ba, idan kuwa haka ne, to mu da wa muke magana a rubuce-rubucenmu? Shin marubutan baya haka suka yi? Yaya tasirin wannan abu yake ga ci gaban mu da al’ummarmu da kuma kasarmu?

2.0 Ko Kafin Ka Ga Biri....
Su kan su Turawan mulkin mallaka sun san irin da Larabci ya yi wa sauran harsunan duniya kafin su durkusar da shi, su maye gurbinsa da nasu, shi ya sa duk inda suka sami kan su a matsayin masu mulkin mallaka, a Afirka ko Asiya ko Amurka ba su yi wasa da cusa tunaninsu da kuma akidojinsu ga al’ummomin da suka ci karo da su ba. Sun yi haka ne da sani, domin ta haka ne kurum za su iya yin zaman darshen a cikin harkokin kasashen da suke yi wa sukuwar salla a wancan lokaci. Shi ya sa tsarin ilimin nasu da littattafan da suka shigo da su domin horaswa, suka kasance cikin harshen ‘yan mallakar, a wasu wurare suka matsa sai a yi komi tamkar a Turai, a wasu wuraren kuwa a kaikaice, wasu kuma ba ka iya bambanta su da masu mulkarsu ta kowace irin fuska, dubi Amurkawa ka kwatanta su da mutanen Indiya ko Pakistan da kuma bakaken fatar Afirka, musamman a tsakanin inda Faransa ta yi turke da kuma inda Birtaniya ta kafa tata lemar. Ma ana, wannan rarrabuwar ita ce ta taimaka wajen gane illar mulkin mallaka da kuma yadda aka rarraba kawuna domin a ji dadin mulki. Bisa wannan tafarki ne Leopord Senghor na Senegal ke nuna bakin cikinsa game da irin ilimin da ya samu ta hanyar Turawan Faransa, yana cewa: A lokacin da nake fafutukar karatu a gida da waje, ‘yan uwana da na bari a gida ba su yi boko ba, sun kasance ‘yan kasa na gari, ni kuwa a kullum da na bar firamare na shiga sakandare, na wuce zuwa jami’a, sai kara hannun riga na yi da al’ummata da kuma kasata. A kullum sai na kara sanin tarihi da yanayin kasashen Turai, ina kuma kara jahilcewa game da tarihin al’ummata da kuma kasata. A lokacin da na dawo gida daga Faransa, sai na ga na kasance bako cikin jama’ata, tsararrakina da na bari ba su yi karatu ba, suka kasance malamaina.

Wannan haka ya kasance dangane da marubuta da shugabanni a nahiyar Afirka, musamman wadanda suka kasance karkashin mulkin Faransa. A bangare daya kuwa, wadanda suka zauna cikin inuwar mulkin Birtaniya ba haka abin ya kasance ba, ga wasu, kamar yadda Mista East ya bayyana game da Abubakar Imam a matsayinsa na marubuci, ya cc:

Ya kasance daya daga cikin ‘yan kalilan da ya kasance duk da cewa ya sami iliminsa ta hanyar horaswa cikin Ingilshi da littattafan Ingilishi, daga kuma Turawan Ingilishi, bai yi watsi da harshensa ba, domin kuwa yana bayyanar da tunaninsa cikin harshen nasa, ba cikin Ingilishi ba kamar yadda saura ke yi.

Me ya bambanta Senghor da Imam? Ba wani abu da ya ya wucc cewa shi Imam bai yarda Ingilishi ya kasance masa harshen tunani ba, ba ma Ingilishi kadai ba, kusan duk wani harshe da ya ci karo da shi a lokacin da yake nadar ilimi da ya gina masa rayuwa. Shi kuwa Senghor ya tashi ne cikin wani tsari da ya fifita tunanin Faranshi bisa na bakar fata, haka al’adu da addini da kuma tsarin ilimin baki daya. Bai sami damar bambance barcin makaho ba ko kuma duma daga kabewa, ba don komi ba kuwa saboda irin yadda ak rene su tun daga gida.

Imam ya sami ilimin addini mai zurfi ko kafin ya hadu da Bature da makircin da ya shigo da shi, saboda haka bai yarda wani makiri ya yi masa wayon wanikiki ba, tun yana karami. Ko da ya shiga dakin ajiyar littatafai na makarantar Midil a Katsina domin ya yi nazarin da zai shiga gasar kaga littattafai da aka shirya a 1933, bai yarda ya yi amfani da duk abin da ya ci karo da shi ba, sai ya karanta, ya auna da abin da addininnmu da kuma tadojinmu na kwarai suka aminta da su, sa’annan yake kattaba shi a cikin nasa aikin, kuma bai taba yarda da tasirin bakin al’adu ko addinai sun ja masa akala ba. Haka su Tabawa Balewa da Ahmadu Bello da Aminu Kano da Sa’adu Zungur da wasu da dama, kuma wannan shi ya haifar da akidar nan ta NEPU da neman canji a wannan yanki da muke ciki.

Bari mu yi bitar wasu daga cikin ayyukan Imam, mu gani ko za mu iya samun haske dangane da irin abubuwan da aka yi a da, kafin mu koma ga shin mu wa muke yi wa rubutu?

3.0 Sai Gida Ya Samu…
A cikin ayyukan da Abubakar ya yi na adabi ba wanda ya zauna ya shirya a cikin ransa da nufin ya nishadantar ko ya burge ko kuma dai a san da shi a cikin harkar rubutu ko kuma rayar da ilimi. Bai yi haka a lokacin rubuta Ruwan Bagaja ba, duk da cewa a lokacin da ya yi rubutun yana da shekara 21 a doron kasa. Ko da ya shiga dakin ajiyar littattafai na makarantarsu domin ya sami samfur na irin yadda zai tsara labarin nasa, ya kuma ci karo da littafin The Water Of Cure na ‘yan uwa Grimms, ba haka nan ya bi shi ya kwashe komi da komi ba kamar yadda labarin yake a kasar Jamus, tun asalinsa, sai da ya bi ya yi masa kwaskwarima ya debe al’adun Jamusawa, ya shigar da na Hausa, ya cire addinin kiristanci ya shigo da Musulunci. Da wannan ne kuma ya shiga cikin littafin Alfu Lailah ya debo hikayar Abdussamad da ‘yan uwansa, ita kuma ya kwashi wani gefe da ya dacc da tunanin malam Bahaushe ya jefa a cikin Ruwan Bagaja, ya yi watsi da tadar Larabawa da ya san cewa ba ta da wani alfanu ga mai karanta Hausa. Ya kuma shiga cikin gonar adabin baka na Hausa inda ya tsamo tatsuniyoyi da labaran Hausa da suka yi tashe a wancan lokaci ya gina zubin littafin. To amma ba inda ya fi fiddo da tsarin kyautatawa fili irin yadda ya nemi Malam Zurke da Alhaji Imam daga rayuwa ta yau da kullum. Shi dai Zurke wani mahaukaci ne da aka yi a cikin birnin Katsina, Alhaji Imam kuwa marubucin ne, amma kuma wadannan mutane a zahiri ya same su ne daga littafin Maqamatul Hariri, inda Harisu da Abu Zaid suka taka rawa irin ta Zurke da Alhaji Imam, sai dai su Harisu dabarun da wayon wanikiki da suka yi a cikin Maqama cike suke da al’adun Larabawa, dole ta sa Imam ya mayar da su na Hausawa, cikin ban dariya da sosa rai

Idan kuma muka dubi Magana Jan Ce (1-3) sai mu ga cewa nan Imam ya nuna gwanancewa fiye da a Ruwan Bagaja, ko ba komi a nan ya san da wa yake magana, ya kuma san dalilin yin rubutun da abin da yake son rubutun nasa ya yi ga wadanda aka yi wa rubutun. Tun da farko, nan ba gasa ba ce, an nemi a yi rubutu ne don yara ‘yan firamare, domin a samar musu abin karatu da kuma tarbiyya. Nan ma Imam sai da ya nemi samfur da zai gina nasa tunanin, amma kamar kullum sai da ya canza wa duk wani tubali da ya tsinto daga wasu wurare sifa ko kuma kama, don su dace da yara ‘yan kasar Hausa. Ya dubi tsarin Alfu Lailah, ya gina budewar Magana Jari Cc, ya kuma yi amfani da littafin The Parrot ya gina batun Aku mai Magana, ya nemo Andersen Fairy Tales da Aesop Fables da Grimms Fairy Tales da kuma tatsuniyoyin Hausa domin su kasance masa ‘ya’yan da ke tafiya da uwar labarin Magana Jari Ce. Ya yi haka ne cikin tunanin makarantarsa, duk inda ya hadu da maganar barayi sai ya yi huduba kan sat da rashin kyan sat, yana kuma bayyana cewa bai son bayar da labarin barayi ba don komi ba sai don gudun kada yara su sami abin kwaikwaya, kuma duk inda ya kawo labarin barayi to bai barin su yi nasara. Kai ba wannan kadai ba, duk inda aka yi mugun abu sai ya nuna horon da aka yi wa wanda ko wadanda suka yi mugun abun, kamar yadda ya fada a cikin tarihinsa, East ya koya masa cewa kada ka yarda ka bar mugu ya yi nasara a cikin gina labarinka, domin tasirin barin haka zai iya rusa al’umma. Wannan shi ne ke cikin zuciyar dukkan ayyukan adabin da Imam ya gina a cikin Magana Jari Ce. Inda ya ji ana maganar itaciyar yeuw (mai kwankwamai) sai ya mayar da ita itaciyar tsamiya. Gidan Turawa na ginin bene, ba zaure don baki da sa kwat da duk wasu abubuwan jin dadi nà rayuwa, irin na Turawa, canza su yake yi da na Hausawa, bai yarda bakon malam Bahaushe ya shigo har cikin gida ba, domin masaukin bako ai zaure ne in ji Hausawa. Haka abinci da abin sha da abin hawa da sauran makamantan su, ba don komi ba sai don wadanda yake wa rubutun su karu da ilimin da ke ciki da kuma inganta kyawawan al’adu.

Imam bai yarda ya bar mugu ya sha ba, bai bar azzalumi ya wuce da zaluncinsa ba, bai kuma bar kunci ya tabbata a cikin rayuwa ba. Duk yadda zai yi ya nuna wa yara kyau da rashin kyawun abu, shi ya bi ya gina tunanin nasa adabin, wannan kuma har yau har kwanan gobe ayyukan nasa suke kasancewa kamar yau ne aka yi su duk da cewa sun yi fiye da shekaru saba’in da da dabbakawa. Darussan da ke ciki har yau suna da tasiri a rayuwar jama’ar yau din ba wa sai na jiyar ba, za su kuma ci gaba da wanzuwa a haka har gobe.

4.0 Kai Wa Kake Wa Rubutu?
Tambayar da kila wasu ke faman yi har yanzu ina jin ba ta wuce to mu wa muke wa rubutu? Kanmu ko gwamnati ko talakawa ko masu ilimi ko kuma madaidaita ilimi ko kuma dai kowa da kowa? Kafin na bayar da wannan amsa, zan so dan mazaya tukun, domin ta haka ne nake jin cewa za mu sami haske game da irin rubutunmu da wadanda muke wa.

Ko da aka gayyace ni da in ce wani abu a wannan taro, na amsa cewa zan zo ne, amma idan an aiko man da takardar gayyata, ba wani abu ya sa na dage kan haka ba sai don ina son in ga inda masu shirya taron suka sa gaba, domin kuwa tun ranar da na cika shekara 40 a watan Oktoban da ya wuce, na sha alwashin cewa ba zan sake mu’amala da Ingilishi ba. Na kuma sha wannan alwashi ne da nufin ganin na bada tawa gudunmuwa wajen kara habaka harshe da adabi da al’adun Hausawa gaba. Ban ce ba na bada gudunmuwa a inda aka fito ba, amma sai na fahimci cewa duk tsawon lokaci muna maganar bebaye ne, ba mai jin abin da muke fada da harshen Ingilishin, ni kuma ga shi ba don neman suna nake abin da nake yi ba.

Taro in na raya adabi ne, rubutu in na raya adabi, magana in ta raya adabi ce, in ni ne zan je ko zan yi ko kuma zan ce, to da Hausa zan yi, sai dai a yi mani aikin gafara.

Da na sami wasikar gayyatar na gan ta cikin Ingilishi sai na ce to wannan ba da ni za a yi ba, karanta takardar ne ya canza mani ra’ayi, domin an ce in yi laccar cikin Hausa, abin da ya kawo ni ke nan.

Kila wasu su ce ai ba sai na bi wannan mataki ba, in yi wake-wake mana, wato in an dama da Ingilishi in sha, in kuma an dama da Hausa in sha. Ba zan iya haka din ba. Ba don komi ba sai don ina son in san wadanda nake wa rubutu. Ba kuma wanda nake wa rubutu face malam Bahaushe. Saboda haka ban ga dalilin da zan zauna ina magana da Bature ba. Ina amfanin badi ba rai.

Kai da ke nan tare da ni a yau wa kake yi wa rubutu? Bahaushe ko Bature? Idan da malam Bahaushe kake magana ko kuma rubutu, to ya dace rubutun nan naka a cikin a cikin jarida ko mujalla ko kagaggen labari ko waka ko kuma wasan kwaikwayo ne ka gwanancc to ya kasance a cikin hasrshen da mutanenka za su gane, za su fahimta, za su kuma yi aiki da shi. A da ban dauki wannan da muhinmanci ba sai da na rubuta From The Eyes Of My Neighbour a 1992, na saki littafin a kasuwa a kan Naira 10 kacal, na rarrabar da dubbai kyauta domin sakon ya kai ga jama’ar da nake jin za su amfana da shi, yau sama da shekara 10 da fitar littafin, ba wanda ya kama ni ko ya ce da ni uffan, duk da cewa zagi da batunci da neman tashin-tashina su ne jibge a cikin littafin. Gwainnatin da wasu ke ganin cewa za ta sa kafar wando da ni ko bihim ba ta ce ba, ba don komi ba sai don wadanda nake bukatar su tashi su yi boren daga zaluncin da ake tafkawa a cikin kasar, ba su ma san da littafin ba. Amma da na rubuta wakar Jigida Ta Ta Tsinke, na rera ta a gaban jama’a a shekarar 1995, ba a yi kwana bakwai ba sai da na yi bakin dare da kuma aka buga a cikin jaridar Nasiha, sai da aka nemi na yi bayani a gaban jami’an tsaro, ba wani abu ya jawo haka ba sai zakin harshen da na yi amfani da shi da kuma damar da harshen yakc da shi na isa ga wadanda ake son bayanin ya isa gare su. A wannan lokaci ne na fara fahimtar wadanda ya kamata in yi wa rubutu na.

Da kurna muka kwashe shekara muna ta hadiyar miyau tsakanina da Abdalla da Sheme sai na fahimci cewa muna jifa ne a cikin duhu, su wadanda ake yi domin su ba su san ana yi ba, idan kuma sun sani, ba abin da za su iya yi, domin dogon Turanci ne kurum ake ta faman yi, domin haka a kai kasuwa. Wannan ma ya sanya man tunani game da shin wa nake yi wa rubutuna.

Saboda haka kai da ke nan wa kake wa rubutu? Mutumin Garun-Ali ko kuma Yorkshire ko Manchester? Kai da ke ta fafutukar rera wakar Ingilishi, kai da ke Ni tsara da kuma aiwatar da wasan kwaikwayo cikin Ingilishi, kai da ke ta faman zayyana labarai cikin Ingilishi, kai da ke ta faman rubutu cikin jarida da harshen Ingilishi, kai da ba ka da abokiyar hira irin jarida ko mujallar Ingilishi ba ruwanka da na Hausa, shin wa kake taimakawa? Malam Mande da ke Kaura-Namoda ko kuma Clement da ke Bradford. Kai da ke faman sai ka wallafa littafi cikin Ingihshi. Don me kake wannan hankoro, domin kedafare ko kuwa don a san ka a Ingila ko Amurka, ba ruwanka da kasar Hausa? Me ya sa kake rubutu? Wa kake wa rubutun? Wace ribar kake nema? Ni dai ba zan ba ka amsa ba, amma na san tawa, sai ka yi tunani, idan mun hadu a wani jikon, zan so in san wa kake wa rubutu? Sai dai fatata ita cc, mu hadu a taron Kungiyar Marubuta Ta Jihar Kano, ba taron ANA ba. Na gode.

No comments: